< Jeremías 15 >

1 Entonces el Señor me dijo: “Aunque Moisés y Samuel estuvieran delante de mí, mi mente no se volvería hacia este pueblo. Apártalos de mi vista y deja que salgan.
Sai Ubangiji ya ce mini, “Ko da Musa da Sama’ila za su tsaya a gabana, zuciyata ba za tă komo ga mutanen nan ba. Ka kore su daga gabana! Su tafi!
2 Sucederá que cuando te pregunten: “¿Por dónde saldremos?”, les dirás: “Dice el Señor: “Los que son para la muerte, a la muerte; los que son para la espada, a la espada; los que son para el hambre, al hambre; y los que son para el cautiverio, al cautiverio”.
In kuma suka tambaye ka, ‘Ina za mu tafi?’ Sai ka faɗa musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Waɗanda aka ƙaddara ga mutuwa, ga mutuwa za su; waɗanda aka ƙaddara ga takobi, ga takobi za su; waɗanda aka ƙaddara ga yunwa, ga yunwa za su; waɗanda aka ƙaddara ga zaman bauta, ga zaman bauta za su.’
3 “Designaré sobre ellos cuatro clases”, dice Yahvé: “la espada para matar, los perros para desgarrar, las aves del cielo y los animales de la tierra para devorar y destruir.
“Zan aika musu da iri masu hallakarwa guda huɗu,” in ji Ubangiji, “takobi zai kashe, karnuka za su kwashe, tsuntsaye da namun jeji kuma su cinye su kuma hallaka.
4 Haré que sean arrojados de un lado a otro entre todos los reinos de la tierra, a causa de Manasés, hijo de Ezequías, rey de Judá, por lo que hizo en Jerusalén.
Zan sa su zama abin ƙyama ga dukan mulkokin duniya saboda abin da Manasse ɗan Hezekiya sarkin Yahuda ya aikata a Urushalima.
5 Porque ¿quién se apiadará de ti, Jerusalén? ¿Quién te llorará? ¿Quién vendrá a preguntar por su bienestar?
“Wa zai ji tausayinki, ya Urushalima? Wa zai yi makoki dominki? Wa zai dakata ya tambayi lafiyarki?
6 Me has rechazado”, dice Yahvé. “Has ido hacia atrás. Por eso he extendido mi mano contra ti y te destruyó. Estoy cansado de mostrar compasión.
Kin ƙi ni,” in ji Ubangiji. “Ki ci gaba da ja da baya. Ta haka zan ɗibiya hannuwana a kanki in hallaka ki; ba zan ƙara nuna miki jinƙai ba.
7 Los he aventado con un abanico en las puertas de la tierra. Les he quitado hijos. He destruido a mi pueblo. No volvieron de sus caminos.
Zan sheƙe ki da abin sheƙewa a ƙofofin birnin ƙasar. Zan kawo baƙin ciki da hallaka a kan mutanena, gama ba su canja hanyoyinsu ba.
8 Sus viudas aumentan más que la arena de los mares. He traído sobre ellos contra la madre de los jóvenes un destructor al mediodía. He hecho que la angustia y los terrores caigan sobre ella de repente.
Zan ƙara yawan gwaurayensu su fi yashin teku yawa. Da tsakar rana zan kawo mai hallakarwa a kan iyaye mata na samarinsu; farat ɗaya zan kawo musu wahala da razana.
9 La que ha dado a luz a siete languidece. Ha renunciado al espíritu. Su sol se ha puesto cuando aún era de día. Se ha sentido decepcionada y confundida. Entregaré sus residuos a la espada ante sus enemigos”, dice Yahvé.
Mahaifiya’ya’ya bakwai za tă suma ta ja numfashinta na ƙarshe. Ranarta zai fāɗi tun lokacin bai yi ba; za tă sha kunya a kuma wulaƙanta ta. Zan sa a kashe raguwa da takobi a gaban abokan gābansu,” in ji Ubangiji.
10 ¡Ay de mí, madre mía, que me has dado a luz, un hombre conflictivo! ¡y un hombre de contención para toda la tierra! Yo no he prestado, ni los hombres me han prestado; pero cada uno de ellos me maldice.
Kaitona, mahaifiyata, da kika haife ni, mutumin da dukan ƙasa take faɗa take kuma gardama da shi! Ban ba da bashi ko in ci bashi ba, duk da haka kowa yana zagina.
11 Yahvé dijo, “Ciertamente te fortaleceré para siempre. Ciertamente haré que el enemigo te suplique en el tiempo del mal y en el tiempo de aflicción.
Ubangiji ya ce, “Tabbatacce zan cece ka don alheri; tabbatacce zan sa abokan gābanka su yi roƙo gare ka a lokacin masifa da kuma lokacin wahala.
12 Se puede romper el hierro, incluso el hierro del norte, y el bronce?
“Mutum zai iya karye ƙarfe ƙarfe daga arewa, ko tagulla?
13 Daré tus bienes y tus tesoros por un botín sin precio, y eso por todos sus pecados, incluso en todas sus fronteras.
“Dukiyarku da arzikinku zan ba da su ganima, babu tara, saboda duka zunubanku ko’ina a ƙasar.
14 Los haré pasar con tus enemigos a una tierra que no conoces; porque un fuego se enciende en mi ira, que arderá en ti”.
Zan bautar da ku ga abokan gābanku a ƙasar da ba ku sani ba, gama fushina zai yi ƙuna kamar wuta da za tă yi ƙuna a kanku.”
15 Yahvé, ya sabes. Recuérdame, visítame, y véngame de mis perseguidores. Eres paciente, así que no me lleves. Sabed que por vosotros he sufrido reproches.
Ka gane, ya Ubangiji; ka tuna da ni ka kuma lura da ni. Ka yi mini ramuwa a kan masu tsananta mini. Cikin jimirinka, kada ka ɗauke ni; ka tuna yadda na sha zagi saboda kai.
16 Sus palabras fueron encontradas, y me los comí. Tus palabras fueron para mí una alegría y el regocijo de mi corazón, porque me llaman por tu nombre, Yahvé, Dios de los Ejércitos.
Sa’ad da maganganunka suka zo, na cinye su; suka zama abin farin ciki zuciyata kuma ta yi murna, gama ana kirana da sunanka, Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki.
17 No me senté en la asamblea de los que se alegran y se regocijan. Me senté solo por tu mano, porque me has llenado de indignación.
Ban taɓa zauna a cikin’yan tawaye ba, ban taɓa yi murna da su ba; na zauna ni kaɗai domin hannunka yana a kaina ka kuma sa na cika da haushi.
18 Por qué mi dolor es perpetuo, y mi herida incurable, que se niega a ser curado? ¿Serás para mí como un arroyo engañoso, ¿como las aguas que fallan?
Me ya sa wahalata ba ta ƙarewa mikina kuma ba ya warkuwa? Za ka zama mini kamar rafi mai yaudara ne, kamar maɓulɓulan da ta kafe ne?
19 Por eso dice Yahvé, “Si vuelves, entonces te traeré de nuevo, para que te presentes ante mí; y si sacas lo precioso de lo vil, serás como mi boca. Volverán a ti, pero no volverás a ellos.
Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “In ka tuba, zan maido da kai don ka bauta mini; in ka ambaci maganganu masu kyau, ba marasa kyau ba, za ka zama kakakina. Bari wannan mutane su juyo gare ka, amma kada ka juye gare su.
20 Haré de ti para este pueblo un muro de bronce fortificado. Lucharán contra ti, pero no prevalecerán contra ti; porque yo estoy con vosotros para salvaros y para liberarte”, dice Yahvé.
Zan mai da kai katanga ga wannan mutane, katanga mai ƙarfi na tagulla; za su yi yaƙi da kai amma ba za su yi nasara a kanka ba, gama ina tare da kai don in kuɓutar in kuma cece ka,” in ji Ubangiji.
21 “Te libraré de la mano de los malvados, y te redimiré de la mano de los terribles”.
“Zan cece ka daga hannuwan mugaye in ɓamɓare ka daga hannun marasa tausayi.”

< Jeremías 15 >