< Jeremías 12 >

1 Tú eres justo, Yahvé, cuando me enfrento a ti; Sin embargo, me gustaría exponer un caso ante usted. ¿Por qué prospera el camino de los malvados? ¿Por qué están tranquilos los que tratan con mucha alevosía?
Kullum kai mai adalci ne, ya Ubangiji, sa’ad da na kawo ƙara a gabanka. Duk da haka zan yi magana da kai game da shari’arka. Me ya sa mugaye suke nasara? Me ya sa dukan maciya amana suke zama ba damuwa?
2 Tú los has plantado. Sí, han echado raíces. Crecen. Sí, producen frutos. Estás cerca de su boca, y lejos de su corazón.
Ka dasa su, sun kuwa yi saiwa; sun yi girma suna ba da’ya’ya. Kullum sunanka yana a bakinsu amma kana nesa da zuciyarsu.
3 Pero tú, Yahvé, me conoces. Me ves, y pruebas mi corazón hacia ti. Sácalos como ovejas para el matadero, y prepararlos para el día de la matanza.
Duk da haka ka san ni, ya Ubangiji; kana ganina ka kuma gwada tunanina game da kai. Ka ja su kamar tumakin da za a yanka! Ka ware su don ranar yanka!
4 Hasta cuándo estará de luto la tierra, ¿y las hierbas de todo el país se marchitan? A causa de la maldad de los que la habitan, los animales y las aves se consumen; porque dijeron, “No verá nuestro último fin”.
Har yaushe ƙasar za tă kasance busasshiya ciyawar kowane fili ta bushe? Domin waɗanda suke zaune cikinta mugaye ne, dabbobi da tsuntsaye sun hallaka. Ban da haka ma, mutane suna cewa, “Ba zai ga abin da yake faruwa da mu ba.”
5 “Si has corrido con los lacayos, y te han cansado, ¿entonces cómo se puede competir con los caballos? Aunque en una tierra de paz estás seguro, pero, ¿cómo lo harás en el orgullo del Jordán?
“In ka yi tsere da mutane a ƙafa suka kuma gajiyar da kai, yaya za ka yi gasa da dawakai? In ka yi tuntuɓe a lafiyayyiyar ƙasa, ƙaƙa za ka yi a kurmin Urdun?
6 Porque incluso tus hermanos, y la casa de tu padre, ¡hasta ellos te han tratado con traición! Incluso ellos han gritado después de ti. No les creas, aunque te digan palabras bonitas.
’Yan’uwanka, iyalinka har su ma sun bashe ka; sun tā da kuka mai ƙarfi a kanka. Kada ka amince da su, ko da yake suna faɗa maganganu masu kyau game da kai.
7 “He abandonado mi casa. He desechado mi herencia. He entregado a la amada de mi alma en manos de sus enemigos.
“Zan yashe gidana, in rabu da gādona; Zan ba da wadda nake ƙauna a hannuwan abokan gābanta.
8 Mi herencia se ha convertido para mí en un león en el bosque. Ella ha pronunciado su voz contra mí. Por eso la he odiado.
Gādona ya zama mini kamar zaki a kurmi. Yana mini ruri; saboda haka na ƙi shi.
9 ¿Es mi herencia como un ave de rapiña moteada? ¿Están las aves de rapiña contra ella por todas partes? Ve, reúne a todos los animales del campo. Tráelos para devorarlos.
Ashe, gādona bai zama mini kamar dabbare dabbaren tsuntsu mai cin nama da sauran tsuntsaye masu cin nama suka kewaye shi da faɗa ba? Tafi ka tattaro dukan namun jeji; ka kawo su su ci.
10 Muchos pastores han destruido mi viña. Han pisoteado mi porción. Han convertido mi agradable porción en un desierto desolado.
Makiyaya masu yawa za su lalace gonar inabina su tattake gonata; za su mai da gonata mai kyau kango marar amfani.
11 La han convertido en una desolación. Me llora, estando desolado. Toda la tierra queda desolada, porque a nadie le importa.
Za tă zama kango, busasshiya da kuma kango a gabana; ƙasar duka za tă zama kango domin ba wanda ya kula.
12 Los destructores han llegado a todas las alturas desnudas del desierto; porque la espada de Yahvé devora desde un extremo de la tierra hasta el otro. Ninguna carne tiene paz.
A kan dukan tsaunukan nan na hamada masu hallakarwa za su zo, gama takobin Ubangiji zai ci daga wannan iyaka ƙasa zuwa wancan; ba wanda zai zauna lafiya.
13 Han sembrado trigo, y han cosechado espinas. Se han agotado, y no se aprovecha nada. Se avergonzarán de sus frutos, a causa de la feroz ira de Yahvé”.
Za su shuka alkama, su girbe ƙayayyuwa; za su gajiyar da kansu, ba za su kuwa sami kome ba. Saboda haka ku sha kunyar abin da kuka girbe saboda zafin fushin Ubangiji.”
14 Dice el Señor: “Con respecto a todos mis malos vecinos, que tocan la herencia que he hecho heredar a mi pueblo Israel: He aquí que yo los arrancaré de su tierra, y arrancaré de entre ellos a la casa de Judá.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Game da dukan mugayen maƙwabtana waɗanda suka ƙwace gādon da na ba wa mutanena Isra’ila kuwa, zan tumɓuke su daga ƙasashensu zan kuma tumɓuke gidan Yahuda daga cikinsu.
15 Sucederá que después de haberlos arrancado, volveré y me compadeceré de ellos. Los haré volver, cada uno a su heredad, y cada uno a su tierra.
Amma bayan na tumɓuke su, zan sāke jin tausayi in komo da kowannensu zuwa gādonsa da kuma ƙasarsa.
16 Sucederá que si aprenden con diligencia los caminos de mi pueblo, para jurar por mi nombre, ‘Vive Yahvé’; así como enseñaron a mi pueblo a jurar por Baal, entonces serán edificados en medio de mi pueblo.
In kuma suka koyi al’amuran mutanena sosai suka kuma yi rantsuwa da sunana, suna cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye’ kamar yadda sun taɓa koya wa jama’ata yin rantsuwa da Ba’al, sa’an nan za su kahu a cikin jama’ata.
17 Pero si no escuchan, entonces arrancaré a esa nación, arrancándola y destruyéndola”, dice Yahvé.
Amma duk al’ummar da ba tă saurara ba, zan tumɓuke ta ɗungum in kuma hallaka ta,” in ji Ubangiji.

< Jeremías 12 >