< Isaías 9 >
1 Pero ya no habrá más tristeza para la que estaba angustiada. En el primer tiempo, despreció la tierra de Zabulón y la tierra de Neftalí; pero en el último tiempo la ha hecho gloriosa, por el camino del mar, al otro lado del Jordán, Galilea de las naciones.
Duk da haka, babu sauran baƙin ciki ga waɗanda suke shan azaba. Dā ya ƙasƙantar da ƙasar kabilan Zebulun da ƙasar Naftali, amma nan gaba zai girmama Galili na Al’ummai, ta hanyar teku wadda take ta Urdun.
2 El pueblo que caminaba en la oscuridad ha visto una gran luz. La luz ha brillado sobre los que vivían en el país de la sombra de la muerte.
Mutanen da suke tafiya cikin duhu sun ga babban haske; a kan waɗanda suke zama a ƙasar inuwar mutuwa haske ya haskaka.
3 Has multiplicado la nación. Has aumentado su alegría. Se alegran ante ti según la alegría de la cosecha, como se alegran los hombres cuando se reparten el botín.
Ka fadada al’umma ka kuma ƙara farin cikinsu; suna farin ciki a gabanka yadda mutane sukan yi murna a lokacin girbi, kamar yadda mutane sukan yi farin ciki sa’ad da suke raba ganima.
4 Porque el yugo de su carga, y el bastón de su hombro, la vara de su opresor, has roto como en el día de Madián.
Gama kamar yadda yake a kwanakin da aka ci Midiyan da yaƙi, kuka ji tsoro nauyin da ya nawaita musu, sandar da yake a kafaɗunsu, sandar masu zaluncinsu.
5 Porque toda la armadura del hombre armado en la batalla ruidosa, y las vestiduras revueltas en sangre, serán para arder, combustible para el fuego.
Kowane takalmin jarumin da aka yi amfani da shi a yaƙi da kuma kowane rigar da ka naɗe cikin jini zai kasance an ƙone shi zai kuma zama abin hura wuta.
6 Porque nos ha nacido un niño. Un hijo se nos ha dado; y el gobierno estará sobre sus hombros. Su nombre será llamado Consejero maravilloso, Dios poderoso, Padre eterno, Príncipe de la paz.
Gama a gare mu an haifa mana yaro, a gare mu an ba da ɗa, gwamnati za tă kasance a kafaɗarsa. Za a ce da shi Mashawarci Mai Banmamaki, Allah Maɗaukaki Uban Madawwami, Sarkin Salama.
7 El aumento de su gobierno y de la paz no tendrá fin, en el trono de David y en su reino, para establecerlo y sostenerlo con justicia y con rectitud desde entonces y para siempre. El celo de Yahvé de los Ejércitos lo llevará a cabo.
Game da girmar gwamnatinsa da salama babu iyaka. Zai gāji sarki Dawuda, yă yi mulki a matsayinsa, zai kafa mulkinsa a kan adalci da gaskiya, tun daga yanzu har zuwa ƙarshen zamani. Ubangiji Maɗaukaki ne ya yi niyyar aikata wannan duka.
8 El Señor envió una palabra a Jacob, y cae sobre Israel.
Ubangiji ya aika da saƙon gāba da Yaƙub; zai auka wa Isra’ila.
9 Todo el pueblo lo sabrá, incluyendo a Efraín y a los habitantes de Samaria, que dicen con orgullo y arrogancia de corazón,
Dukan mutane za su san shi, Efraim da mazaunan Samariya, waɗanda suke magana da fariya suna kuma ɗaga kai,
10 “Los ladrillos han caído, pero construiremos con piedra cortada. Las higueras de sicomoro han sido cortadas, pero pondremos cedros en su lugar”.
“Tubalai sun zube a ƙasa, amma za mu sāke gina su da dutse; an sassare itatuwan ɓaure, amma za mu maya su da al’ul.”
11 Por lo tanto, Yahvé pondrá en alto a los adversarios de Rezín, y agitará a sus enemigos,
Amma Ubangiji ya ƙarfafa maƙiyan Rezin gāba da su ya kuma ingiza abokan gāba.
12 Los sirios al frente, y los filisteos detrás; y devorarán a Israel con la boca abierta. Por todo esto, su ira no se desvía, pero su mano está extendida todavía.
Arameyawa daga gabas da Filistiyawa daga yamma sun cinye Isra’ila da buɗaɗɗen baki. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
13 Sin embargo, el pueblo no se ha vuelto hacia el que lo golpeó, ni han buscado a Yahvé de los Ejércitos.
Amma mutanen ba su juyo wurin wanda ya buge su ba, balle su nemi Ubangiji Maɗaukaki.
14 Por eso el Señor cortará de Israel la cabeza y la cola, rama de palma y caña, en un día.
Saboda haka Ubangiji zai yanke Isra’ila kai da wutsiya, da reshen dabino da iwa a rana guda;
15 El hombre mayor y honorable es la cabeza, y el profeta que enseña la mentira es la cola.
dattawa da manyan mutane su ne kai, annabawa waɗanda suke koyar da ƙarairayi su ne wutsiya.
16 Porque los que guían a este pueblo lo extravían; y los que son guiados por ellos son destruidos.
Waɗanda suke jagorar wannan mutane suna ɓad da su, su ne waɗanda ake jagora aka sa suka kauce.
17 Por eso el Señor no se alegrará de sus jóvenes, ni tendrá compasión de sus huérfanos y viudas; porque todos son profanos y malhechores, y toda boca habla con locura. Por todo esto su ira no se desvía, pero su mano está extendida todavía.
Saboda haka Ubangiji ba zai ji daɗin matasa ba, ba kuwa zai ji tausayin marayu da gwauraye ba, gama kowa marar sanin Allah ne da kuma mugu, kowane baki yana faɗin mugayen maganganu. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
18 Porque la maldad arde como el fuego. Devora las zarzas y las espinas; sí, se enciende en la espesura del bosque, y ruedan hacia arriba en una columna de humo.
Tabbatacce mugunta tana ƙuna kamar wuta; tana cin ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya, ta sa wuta a jeji mai itatuwa masu yawa, don yă yi murtuke hayaƙi har zuwa sama.
19 Por la ira de Yahvé de los Ejércitos, la tierra es quemada; y la gente es el combustible para el fuego. Nadie perdona a su hermano.
Ta wurin fushin Ubangiji Maɗaukaki ƙasar za tă ci wuta mutane kuma za su zama abin hura wutar, babu wanda zai ji tausayin ɗan’uwansa.
20 Uno devorará a la derecha y tendrá hambre; y comerá a la izquierda, y no quedarán satisfechos. Cada uno comerá la carne de su propio brazo:
A dama za su ci, amma su ci gaba da jin yunwa; a hagu za su ci, amma ba za su ƙoshi ba. Kowa zai mai da naman’ya’yansa abinci.
21 Manasés comiendo a Efraín y Efraín comiendo a Manasés, y juntos estarán contra Judá. Por todo esto su ira no se desvía, pero su mano está extendida todavía.
Manasse zai mai da Efraim abinci, Efraim kuma yă cinye Manasse; tare za su yi gāba da Yahuda. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.