< Isaías 60 >
1 “Levántate, brilla, porque ha llegado tu luz, y la gloria de Yahvé se ha levantado sobre ti.
“Ki tashi, ki haskaka, gama haskenki ya zo, ɗaukakar Ubangiji ya taso a kanki.
2 Porque he aquí que las tinieblas cubrirán la tierra, y espesa oscuridad los pueblos; pero Yahvé se levantará sobre ti, y su gloria se verá en ti.
Duba, duhu ya rufe duniya duhu mai kauri kuma yana bisa mutane, amma Ubangiji ya taso a kanki ɗaukakarsa kuma ya bayyana a bisanki.
3 Las naciones vendrán a tu luz, y los reyes al brillo de su ascenso.
Al’ummai za su zo wurin haskenki, sarakuna kuma zuwa asubahin sabon yininki.
4 “Alza los ojos a tu alrededor y mira: todos se reúnen. Vienen a ti. Sus hijos vendrán de lejos, y sus hijas serán llevadas en brazos.
“Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye da ke. Duka sun tattaru suka kuma zo wurinki;’ya’yanki maza daga nesa, ana kuma ɗaukan’ya’yanki mata a hannu.
5 Entonces verás y estarás radiante, y tu corazón se estremecerá y se ensanchará; porque la abundancia del mar se volverá hacia ti. La riqueza de las naciones vendrá a ti.
Sa’an nan za ki duba ki kuma haskaka zuciyarki zai motsa ya kuma cika da farin ciki; za a kawo miki wadata daga tekuna, za a kawo miki arzikin al’ummai.
6 Una multitud de camellos te cubrirá, los dromedarios de Madián y Efá. Todos los de Saba vendrán. Traerán oro e incienso, y proclamarán las alabanzas de Yahvé.
Manyan ayarin raƙuma za su cika ƙasar, ƙananan raƙuma ke nan daga Midiyan da Efa. Daga Sheba kuma duka za su zo, suna ɗauke da zinariya da turare suna shelar yabon Ubangiji.
7 Todos los rebaños de Cedar se reunirán contigo. Los carneros de Nebaioth te servirán. Serán aceptados como ofrendas en mi altar; y embelleceré mi gloriosa casa.
Dukan garkunan Kedar za su taru a wurinki ragunan Nebayiwot za su yi miki hidima; za a karɓe su kamar hadayu a kan bagadenki, zan kuma darjanta haikalina mai ɗaukaka.
8 “¿Quiénes son esos que vuelan como una nube? y como las palomas a sus ventanas?
“Su wane ne waɗannan da suke firiya kamar gizagizai, kamar kurciyoyi suna zuwa sheƙarsu?
9 Seguramente las islas me esperarán, y los barcos de Tarsis primero, para traer a tus hijos desde muy lejos, su plata y su oro con ellos, por el nombre de Yahvé, tu Dios, y para el Santo de Israel, porque te ha glorificado.
Babu shakka tsibirai suna dogara gare ni; jiragen Tarshish kuma su ne a gaba, suna kawo’ya’yanki maza daga nesa, tare da azurfa da zinariya, domin su girmama Ubangiji Allahnki, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya cika ki da daraja.
10 “Los extranjeros construirán sus muros, y sus reyes te servirán; porque en mi ira te golpeé, pero en mi favor he tenido misericordia de ti.
“Baƙi za su sāke gina katangarki, sarakunansu kuma za su yi miki hidima. Ko da yake a cikin fushi na buge ki, da tagomashi zan yi miki jinƙai.
11 Tus puertas estarán siempre abiertas; no se cerrarán ni de día ni de noche, para que los hombres traigan a ti las riquezas de las naciones, y sus reyes sean llevados cautivos.
Ƙofofinki kullum za su kasance a buɗe, ba za a ƙara rufe su da rana ko da dare ba, saboda mutane su kawo miki dukiyar al’ummai, sarakunansu za su kasance a gaba a jerin gwanon nasara.
12 Porque la nación y el reino que no te sirvan, perecerán; sí, esas naciones serán totalmente desechas.
Gama al’umma ko masarautar da ba tă bauta miki ba, za tă hallaka; za tă lalace sarai.
13 “La gloria del Líbano vendrá a ti, el ciprés, el pino y el boj juntos, para embellecer el lugar de mi santuario; y haré glorioso el lugar de mis pies.
“Darajar Lebanon za tă zo wurinki, itatuwan fir da dai ire-irensu da kuma itatuwan saifires duka za su zo don su ƙayatar da wurina mai tsarki; zan kuma ɗaukaka wurin ƙafafuna.
14 Los hijos de los que te afligieron vendrán a inclinarse ante ti; y todos los que te despreciaron se postrarán a las plantas de tus pies. Te llamarán Ciudad de Yahvé, la Sión del Santo de Israel.
’Ya’ya maza masu zaluntarku za su zo suna rusunawa a gabanki; dukan waɗanda suka rena ki za su rusuna a ƙafafunki su kuma ce da ke Birnin Ubangiji, Sihiyona na Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
15 “Mientras que tú has sido abandonado y odiado, para que nadie pase por ti, Te haré una excelencia eterna, una alegría de muchas generaciones.
“Ko da yake an yashe ki aka kuma ƙi ki, har babu wani da ya ratsa a cikinki, zan mai da ke madawwamiyar abar taƙama da kuma farin cikin dukan zamanai.
16 También beberás la leche de las naciones, y se amamantará de los pechos reales. Entonces sabrás que yo, Yahvé, soy tu Salvador, tu Redentor, el Poderoso de Jacob.
Za ki sha madarar al’ummai a kuma shayar da ke da nonon sarauta. Sa’an nan za ki san cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Mai Ikon nan na Yaƙub.
17 Para el bronce traeré oro; por el hierro traeré plata; para la madera, el bronce, y para las piedras, el hierro. También haré de la paz su gobernador, y la justicia tu gobernante.
A maimakon tagulla zan kawo zinariya, azurfa kuma a maimakon baƙin ƙarfe. A maimakon katako zan kawo tagulla, baƙin ƙarfe kuma a maimakon duwatsu. Zan sa salama ta zama gwamnarki adalci kuma mai mulkinki.
18 No se oirá más la violencia en tu tierra, ni desolación ni destrucción dentro de tus fronteras; pero tú llamarás a tus muros Salvación, y sus puertas Alabanza.
Ba za a ƙara jin hayaniyar tashin hankali a ƙasarki ba, balle lalacewa ko hallaka a cikin iyakokinki, amma za ki kira katangarki Ceto ƙofofinki kuma Yabo.
19 El sol ya no será tu luz de día, ni el brillo de la luna te alumbrará, pero Yahvé será su luz eterna, y tu Dios será tu gloria.
Rana ba za tă ƙara zama haskenki a yini ba, balle hasken wata ya haskaka a kanki, gama Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, Allahnki kuma zai zama ɗaukakarki.
20 Tu sol no se pondrá más, ni su luna se retirará; porque Yahvé será tu luz eterna, y los días de tu luto terminarán.
Ranarki ba za tă ƙara fāɗuwa ba watanki kuma ba zai ƙara shuɗewa ba; Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, kwanakin baƙin cikinki za su ƙare.
21 Entonces todo tu pueblo será justo. Heredarán la tierra para siempre, la rama de mi plantación, el trabajo de mis manos, para que yo sea glorificado.
Sa’an nan dukan mutanenki za su zama masu adalci za su kuma mallaki ƙasar har abada. Su ne reshen da na shuka, aikin hannuwana, don nuna darajata.
22 El pequeño se convertirá en mil, y la pequeña una nación fuerte. Yo, Yahvé, haré esto rápidamente en su momento”.
Mafi ƙanƙanta a cikinki za tă zama dubu, ƙarami zai zama al’umma mai girma. Ni ne Ubangiji, cikin lokacinsa zan yi haka da sauri.”