< Isaías 53 >

1 ¿Quién ha creído en nuestro mensaje? ¿A quién se le ha revelado el brazo de Yahvé?
Wa ya gaskata saƙonmu kuma ga wa hannun Ubangiji ya bayyana?
2 Porque creció ante él como una planta tierna, y como una raíz de la tierra seca. No tiene buen aspecto ni majestuosidad. Cuando lo vemos, no hay belleza que nos haga desearlo.
Ya yi girma kamar dashe marar ƙarfi, kamar saiwa kuma daga ƙeƙasasshiyar ƙasa. Ba shi da kyan gani ko wani makamin da zai ja hankalinmu, babu wani abin da yake da shi da zai sa mu yi sha’awarsa.
3 Fue despreciado y rechazada por los hombres, un hombre que sufre y familiarizado con la enfermedad. Fue despreciado como alguien de quien los hombres ocultan su rostro; y no lo respetamos.
Mutane suka rena shi suka ƙi shi, mutum ne cike da baƙin ciki, ya kuma saba da wahala. Kamar wanda mutane suna ɓuya fuskokinsu daga gare shi aka rena shi aka yi banza da shi.
4 Ciertamente ha soportado nuestra enfermedad y llevó nuestro sufrimiento; sin embargo, lo consideramos plagado, golpeado por Dios, y afligido.
Tabbatacce ya ɗauki cututtukanmu ya kuma daure da baƙin cikinmu duk da haka muka ɗauka Allah ya hukunta shi ne, ya buge shi ya kuma sa ya sha azaba.
5 Pero fue traspasado por nuestras transgresiones. Fue aplastado por nuestras iniquidades. El castigo que trajo nuestra paz estuvo en él; y por sus heridas quedamos curados.
Amma aka yi masa rauni saboda laifofinmu, aka ƙuje shi saboda kurakuranmu; hukuncin da ya kawo mana salama ya kasance a kansa, kuma ta wurin mikinsa ya sa muka warke.
6 Todos nosotros, como ovejas, nos hemos extraviado. Cada uno se ha vuelto a su manera; y Yahvé ha hecho recaer sobre él la iniquidad de todos nosotros.
Dukanmu, muna kama da tumakin da suka ɓata, kowannenmu ya kama hanyarsa; Ubangiji kuwa ya sa hukunci ya auko a kansa hukuncin da ya wajaba a kanmu.
7 Estaba oprimido, sin embargo, cuando fue afligido no abrió la boca. Como un cordero que es llevado al matadero, y como una oveja que ante sus esquiladores calla, así que no abrió la boca.
Aka wulaƙanta shi aka kuma yi masa azaba, duk da haka bai buɗe bakinsa ba; aka kai shi kamar ɗan rago zuwa wurin yanka, kuma kamar tunkiya a gaban masu askinta tana shiru, haka bai buɗe bakinsa ba.
8 Fue llevado por la opresión y el juicio. En cuanto a su generación, que consideraba que había sido eliminado de la tierra de los vivos y golpeado por la desobediencia de mi pueblo?
Da wulaƙanci da kuma hukunci aka ɗauke shi aka tafi. Wa kuwa zai yi maganar zuriyarsa? Gama an kawar da shi daga ƙasar masu rai; saboda laifin mutanena aka kashe shi.
9 Hicieron su tumba con los malvados, y con un hombre rico en su muerte, aunque no había ejercido ninguna violencia, ni hubo engaño en su boca.
Aka yi jana’izarsa tare da mugaye, aka binne shi tare da masu arziki, ko da yake bai taɓa yin wani tashin hankali ba, ko a sami ƙarya a bakinsa.
10 Sin embargo, a Yahvé le agradó herirlo. Le ha hecho sufrir. Cuando haces de su alma una ofrenda por el pecado, verá a su descendencia. Prolongará sus días y la voluntad de Yahvé prosperará en su mano.
Duk da haka nufin Ubangiji ne a ƙuje shi yă kuma sa yă sha wahala, kuma ko da yake Ubangiji ya sa ransa ya zama hadaya don zunubi, zai ga zuriyarsa zai kuma kawo masa tsawon rai, nufin Ubangiji kuma zai yi nasara a hannunsa.
11 Tras el sufrimiento de su alma, verá la luz y estará satisfecho. Mi siervo justo justificará a muchos por el conocimiento de sí mismo; y cargará con sus iniquidades.
Bayan wahalar ransa, zai ga hasken rai, ya kuma gamsu; ta wurin saninsa bawana mai adalci zai’yantar da mutane masu yawa, zai kuma ɗauki laifofinsu.
12 Por eso le daré una parte con los grandes. Repartirá el botín con los fuertes, porque derramó su alma hasta la muerte y fue contado con los transgresores; pero llevó los pecados de muchos e intercedió por los transgresores.
Saboda haka zan ba shi rabo tare da manya, zai kuma raba ganima tare da masu ƙarfi, domin ya ba da ransa har mutuwa, aka kuma lissafta shi tare da masu laifofi. Gama ya ɗauki zunubin mutane masu yawa, ya kuma yi roƙo saboda laifofinsu.

< Isaías 53 >