< Isaías 45 >

1 Yahvé dice a su ungido, a Ciro, cuya mano derecha he sostenido para someter a las naciones ante él y despojar a los reyes de sus armaduras, que abra las puertas ante él, y que las puertas no se cierren:
“Ga abin da Ubangiji ya faɗa wa shafaffensa, ga Sairus, wanda hannun damansa yana riƙe da shi don yă ci al’ummai a gabansa ya kuma tuɓe makaman sarakuna, don yă buɗe ƙofofi a gabansa don kada a kulle ƙofofi.
2 “Iré delante de ti y alisar las asperezas. Romperé las puertas de bronce en pedazos y cortar las barras de hierro.
Zan sha gabanka in baje duwatsu; zan farfashe ƙofofin tagulla in kuma kakkarye ƙyamaren ƙarfe.
3 Te daré los tesoros de la oscuridad y las riquezas ocultas de los lugares secretos, para que sepas que soy yo, Yahvé, quien te llama por tu nombre, el Dios de Israel.
Zan ba ka dukiyar duhu, arzikin da aka ajiye a asirtattun wurare, saboda ka san cewa ni ne Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya kira ka da suna.
4 Por el bien de Jacob, mi siervo, e Israel mis elegidos, Te he llamado por tu nombre. Te he dado un título, aunque no me hayas conocido.
Saboda sunan Yaƙub bawana, Isra’ila zaɓaɓɓena, na kira ka da suna na ba ka matsayin bangirma, ko da yake ba ka san ni ba.
5 Yo soy Yahvé, y no hay nadie más. Además de mí, no hay ningún Dios. Te fortaleceré, aunque no me hayas conocido,
Ni ne Ubangiji, kuma babu wani; in ban da ni babu wani Allah. Zan ƙarfafa ka, ko da yake ba ka san ni ba,
6 para que sepan desde la salida del sol, y desde el oeste, que no hay nadie más que yo. Yo soy Yahvé, y no hay nadie más.
saboda daga fitowar rana har zuwa fāɗuwarta mutane za su san cewa babu wani in ban da ni. Ni ne Ubangiji, kuma babu wani.
7 Formo la luz y crear oscuridad. Hago las paces y crear calamidades. Yo soy Yahvé, que hace todas estas cosas.
Ni ne na siffanta haske na kuma halicci duhu, ni ne nake ba da nasara in kuma jawo bala’i; ni, Ubangiji ne ke aikata dukan waɗannan abubuwa.
8 Llueve, cielos, desde arriba, y que los cielos derramen justicia. Que la tierra se abra, para que produzca la salvación, y que haga brotar la justicia con ella. Yo, Yahvé, lo he creado.
“Ku sammai, ku sauko da adalci kamar ruwan sama; bari gizagizai su zubar da yayyafi kamar adalci. Bari ƙasa ta buɗe, bari ceto ya tsiro, bari adalci ya yi girma tare da shi; ni, Ubangijine, na sa ya faru.
9 Ay de aquel que lucha con su Hacedor — ¡una olla de barro entre las ollas de barro de la tierra! ¿Preguntará el barro al que lo moldea: “Qué estás haciendo”? o su trabajo, ‘No tiene manos’?
“Kaitonka mai gardama da Wanda ya yi ka, da wanda yake kasko a cikin kasko a ƙasa. Yumɓu ya iya ce wa magini, ‘Me kake yi?’ Aikinka na iya cewa, ‘Ba shi da hannuwa’?
10 Ay del que diga a un padre: “¿De qué te has convertido en padre?”. o a una madre: “¿Qué has dado a luz?”
Kaiton wanda yake cewa mahaifinsa, ‘Me ka manta?’ Ko kuwa ga mahaifiyarsa, ‘Me kin haifa?’
11 Yahvé, el Santo de Israel y su Hacedor dice: “Me preguntas sobre las cosas que están por venir, sobre mis hijos, ¡y tú me mandas sobre la obra de mis manos!
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, da kuma Mahaliccinsa. Game da abubuwan da ke zuwa, kun tambaye ni game da’ya’yana, ko kuwa kun ba ni umarni game da aikin hannuwana?
12 Yo hice la tierra y creé al hombre sobre ella. Yo, hasta mis manos, he extendido los cielos. He comandado todo su ejército.
Ai, ni ne wanda ya yi duniya na kuma halicci mutum a kanta. Hannuwana ne sun miƙe sammai; na umarci rundunar sararin sama.
13 Yo lo he resucitado en la justicia, y enderezaré todos sus caminos. Él construirá mi ciudad, y dejará libres a mis exiliados, no por precio ni por recompensa”, dice Yahvé de los Ejércitos.
Zan tā da Sairus cikin adalcina. Zan sa dukan hanyoyinsa su miƙe. Zai sāke gina birnina ya kuma’yantar da mutanena masu bautar talala, amma ba don wata haya ko lada ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
14 Yahvé dice: “El trabajo de Egipto, y las mercancías de Etiopía, y los sabeos, hombres de talla, se acercarán a ti, y serán tuyos. Irán a por ti. Vendrán encadenados. Se inclinarán ante ti. Te harán una súplica: Ciertamente, Dios está en ti, y no hay nadie más. No hay otro dios.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kayayyakin Masar da hajar Kush, da waɗannan dogayen Sabenawa, za su ƙetaro zuwa wurinku za su kuma zama naku; za su bi bayanku, suna zuwa cikin sarƙoƙi. Za su rusuna a gabanku su roƙe ku, suna cewa, ‘Tabbas Allah yana tare da ku, babu kuma wani; babu wani allah.’”
15 Ciertamente eres un Dios que se ha escondido, Dios de Israel, el Salvador”.
Tabbatacce kai ne Allah wanda ya ɓoye kanka, Ya Allah da Mai Ceton Isra’ila.
16 Se sentirán decepcionados, sí, confundidos, todos ellos. Los que son fabricantes de ídolos irán juntos a la confusión.
Dukan masu yin gumaka za su sha kunya; za su fita da kunya gaba ɗaya.
17 Israel será salvado por Yahvé con una salvación eterna. No serás defraudado ni confundido por los siglos de los siglos.
Amma Ubangiji zai ceci Isra’ila da madawwamin ceto; ba za ku sāke shan kunya ko ƙasƙanci ba, har abada.
18 Porque Yahvé, que creó los cielos, el Dios que formó la tierra y la hizo, que lo estableció y no lo creó un desperdicio, que lo formó para ser habitado dice: “Yo soy Yahvé. No hay otra.
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicci sammai, shi ne Allah; shi da ya sarrafa ya kuma yi duniya, ya kafa ta; bai halicce ta don ta zama ba kome ba, amma ya yi ta don a zauna a ciki, ya ce, “Ni ne Ubangiji, kuma babu wani.
19 No he hablado en secreto, en un lugar de la tierra de las tinieblas. No he dicho a la descendencia de Jacob: “Buscadme en vano”. Yo, Yahvé, hablo de justicia. Declaro cosas que son correctas.
Ban yi magana asirce ba, daga wani wuri a ƙasar duhu ba; ban faɗa wa zuriyar Yaƙub, ‘Ku neme ni a banza ba.’ Ni, Ubangiji maganar gaskiya nake yi; na furta abin da yake daidai.
20 “Reúnanse y vengan. Acercaos juntos, los que habéis escapado de las naciones. No tienen conocimiento los que llevan la madera de su imagen grabada, y rezar a un dios que no puede salvar.
“Ku tattaru ku zo; ku taru, ku masu gudun hijira daga al’ummai. Masu jahilci ne waɗanda suke ɗaukan gumakan katakai suna yawo, waɗanda suke addu’a ga allolin da ba za su cece su ba.
21 Decláralo y preséntalo. Sí, que se asesoren juntos. ¿Quién lo ha demostrado desde la antigüedad? ¿Quién lo ha declarado de antiguo? ¿No es así, Yahvé? No hay otro Dios más que yo, un Dios justo y un Salvador. No hay nadie más que yo.
Furta abin da zai kasance, ku gabatar da shi, bari su yi shawara tare. Wa ya faɗa wannan tuntuni, wa ya yi shelar sa a kwanakin dā? Ba ni ba ne, Ubangiji? Kuma babu Allah in ban da ni, Allah mai adalci da kuma Mai Ceto; babu wani sai ni.
22 “Miradme y salvaos, todos los confines de la tierra; porque yo soy Dios y no hay otro.
“Ku juyo gare ni ku sami ceto, dukanku iyakokin duniya; gama ni ne Allah, kuma babu wani.
23 He jurado por mí mismo. La palabra ha salido de mi boca en justicia, y no será revocada, que ante mí se doblará toda rodilla, toda lengua prestará juramento.
Da kaina na rantse, bakina ya furta cikin dukan mutunci kalmar da ba za a janye ba. A gabana kowace gwiwa za tă durƙusa; ta wurina kowane harshe zai rantse.
24 Dirán de mí, ‘Sólo en Yahvé hay justicia y fuerza’”. Incluso a él vendrán los hombres. Todos los que se ensañaron con él se sentirán decepcionados.
Za su yi zance game da ni su ce, ‘A cikin Ubangiji kaɗai akwai adalci da kuma ƙarfafawa.’” Duk wanda ya yi fushi da shi zai zo wurinsa ya kuma sha kunya.
25 Toda la descendencia de Israel será justificada en Yahvé, y se alegrará.
Amma a cikin Ubangiji dukan zuriyar Isra’ila za su sami adalci za su kuwa yi yabo.

< Isaías 45 >