< Isaías 26 >

1 En aquel día se cantará esta canción en la tierra de Judá: “Tenemos una ciudad fuerte. Dios designa la salvación para los muros y los baluartes.
A wannan rana za a rera wannan waƙa a ƙasar Yahuda. Muna da birni mai ƙarfi; Allah yake ceton katanga da kuma kagarunta.
2 Abrid las puertas para que entre la nación justa: el que mantiene la fe.
A buɗe ƙofofi saboda al’umma mai adalci ta shiga, al’ummar da mai aminci.
3 Mantendrás la mente del que esté firme en perfecta paz, porque confía en ti.
Za ka kiyaye shi da cikakken salama shi wanda ya kafa zuciyarsa gare ka, domin ya dogara a gare ka.
4 Confía en Yahvé para siempre; porque en Yah, Yahvé, hay una Roca eterna.
Ku dogara ga Ubangiji, gama shi Ubangiji, ne madawwamin Dutse.
5 Porque ha derribado a los que habitan en las alturas, la ciudad elevada. Lo pone bajo. Lo pone bajo incluso hasta el suelo. Lo lleva hasta el polvo.
Yakan ƙasƙantar da waɗanda suke zama a bisa ya kawar da birni mai alfarma ƙasa; ya rusa ta har ƙasa ya jefar da ita cikin ƙura.
6 El pie lo pisará, hasta los pies de los pobres y los pasos de los necesitados”.
Ƙafafu sukan tattake ta, ƙafafu waɗanda aka zalunta, wato, sawun matalauta.
7 El camino del justo es la rectitud. Tú, que eres recto, haces que el camino de los justos sea llano.
Hanyar masu adalci sumul take; Ya Mai Aikata Gaskiya, ka sa hanyar masu adalci ta yi sumul.
8 Sí, en el camino de tus juicios, Yahvé, te hemos esperado. Tu nombre y tu fama son el deseo de nuestra alma.
I, Ubangiji, cikin tafiya a hanyar dokokinka, muna sa zuciya gare ka; sunanka da tunani a kanka su ne marmarin zukatanmu.
9 Con mi alma te he deseado en la noche. Sí, con mi espíritu dentro de mí te buscaré con ahínco; porque cuando tus juicios están en la tierra, los habitantes del mundo aprenden la justicia.
Raina yana marmarinka da dare; da safe kuma raina yana son ganinka. Sa’ad da hukunce-hukuncenka suka sauko duniya, mutanen duniya kan koyi adalci.
10 Que se muestre el favor a los malvados, pero no aprenderá la justicia. En la tierra de la rectitud hará un trato incorrecto, y no verán la majestad de Yahvé.
Ko da yake akan nuna wa mugaye alheri, ba sa koyi adalci; har ma a ƙasar masu aikata gaskiya sukan ci gaba da aikata mugunta ba sa ganin girmar darajar Ubangiji.
11 Yahvé, tu mano está levantada, pero ellos no ven; pero verán tu celo por el pueblo y se decepcionarán. Sí, el fuego consumirá a tus adversarios.
Ya Ubangiji an ɗaga hannunka sama, amma ba sa ganinsa. Bari su ga himmarka don mutanenka su kuma sha kunya; bari wutar da aka ajiye don abokan gābanka ta cinye su.
12 Yahvé, tú ordenarás la paz para nosotros, ya que tú también has hecho todo nuestro trabajo por nosotros.
Ubangiji ka kafa salama dominmu; duk abin da muka iya yi kai ne ka yi mana.
13 Yahvé, nuestro Dios, otros señores, además de ti, se han enseñoreado de nosotros, pero sólo reconoceremos su nombre.
Ya Ubangiji, Allahnmu, waɗansu iyayengiji ban da kai sun yi mulki a kanmu, amma sunanka kaɗai muka girmama.
14 Los muertos no vivirán. Los espíritus difuntos no se levantarán. Por eso los has visitado y destruido, y ha hecho perecer todo recuerdo de ellos.
Yanzu duk sun mutu, ba za su ƙara rayuwa ba; waɗannan ruhohin da suka rasu ba za su tashi ba. Ka hukunta su ka kuma kawo su ga hallaka; ka sa ba za a ƙara tunawa da su ba.
15 Tú has aumentado la nación, oh Yahvé. ¡Has aumentado la nación! ¡Estás glorificado! Has ampliado todas las fronteras de la tierra.
Ka fadada al’umma, ya Ubangiji; ka fadada al’umma. Ka samo wa kanka ɗaukaka; ka fadada dukan iyakokin ƙasar.
16 Yahvé, en la angustia te han visitado. Derramaron una oración cuando su castigo estaba sobre ellos.
Ubangiji, sun zo gare ka a cikin damuwarsu; sa’ad da ka hore su, da ƙyar suna iya yin addu’a.
17 Como una mujer embarazada, que se acerca al momento del parto, está en el dolor y grita en sus dolores, así hemos estado ante ti, Yahvé.
Kamar mace mai ciki da take gab da haihuwa takan yi ta murɗawa tana kuka saboda zafi, haka muka kasance a gabanka, ya Ubangiji.
18 Hemos estado con el niño. Hemos sufrido. Parece que sólo hemos dado a luz al viento. No hemos obrado ninguna liberación en la tierra; tampoco han caído los habitantes del mundo.
Muna da ciki, mun yi ta murɗewa saboda zafi, amma mun haifi iska. Ba mu kawo ceto ga duniya ba; ba mu haifi mutanen duniya ba.
19 Tus muertos vivirán. Sus cadáveres se levantarán. Despierta y canta, tú que habitas en el polvo; porque tu rocío es como el rocío de las hierbas, y la tierra expulsará a los espíritus difuntos.
Amma matattunka za su rayu; jikunansu za su tashi. Ku da kuke zama a ƙura, ku farka ku kuma yi sowa don farin ciki. Raɓarka kamar raɓar safiya ce; duniya za tă haifi matattunta.
20 Venid, pueblo mío, entrad en vuestras habitaciones, y cerrar las puertas detrás de ti. Escóndete por un momento, hasta que pase la indignación.
Ku tafi, mutanena, ku shiga ɗakunanku ku kuma kulle ƙofofi; ku ɓoye kanku na ɗan lokaci sai ya huce fushinsa.
21 Porque he aquí que Yahvé sale de su lugar para castigar a los habitantes de la tierra por su iniquidad. La tierra también revelará su sangre, y ya no cubrirá a sus muertos.
Duba, Ubangiji yana fitowa daga mazauninsa don yă hukunta mutanen duniya saboda zunubansu. Duniya za tă bayyana zub da jinin da aka yi a kanta; ba za tă ƙara ɓoye waɗanda aka kashe a cikinta ba.

< Isaías 26 >