< Isaías 15 >

1 La carga de Moab. Porque en una noche, Ar de Moab es asolada, y reducida a la nada. Porque en una noche Kir de Moab es asolada y reducida a la nada.
Abin da Allah ya yi magana a kan Mowab shi ne, An lalatar da Ar a Mowab, an hallaka ta da dare! An lalatar da Kir a Mowab, an hallaka ta da dare!
2 Subieron a Bayit y a Dibón, a los lugares altos, para llorar. Moab se lamenta sobre Nebo y sobre Medeba. La calvicie está en todas sus cabezas. Todas las barbas están cortadas.
Dibon ya haura zuwa haikalinta, zuwa masujadan kan tudu don tă yi kuka; Mowab ta yi ihu a kan Nebo da Medeba. An aske kowane kai an kuma yanke kowane gemu.
3 En sus calles se visten de cilicio. En sus calles y en las azoteas, todos se lamentan, llorando abundantemente.
A tituna sun sa tsummoki a jikunansu; a kan rufin ɗakuna da kuma dandalin taruwa dukansu sai makoki suke yi, sun kwanta suna kuka.
4 Hesbón grita con Elealeh. Su voz se oye hasta Jahaz. Por eso los hombres armados de Moab gritan en voz alta. Sus almas tiemblan dentro de ellos.
Heshbon da Eleyale sun yi kuka da ƙarfi, aka ji muryoyinsu ko’ina har zuwa Yahaz. Saboda haka mayaƙan Mowab suka yi kuka da ƙarfi, har zuciyarsu ta karai.
5 ¡Mi corazón clama por Moab! Sus nobles huyen a Zoar, a Eglath Shelishiyah; porque suben por la subida de Luhit con llanto; porque en el camino a Horonaim, lanzan un grito de destrucción.
Zuciyata ta yi kuka a kan Mowab; mutanenta sun gudu har zuwa Zowar, har zuwa Eglat Shelishiya. Sun haura zuwa Luhit, suna tafe suna kuka; a kan hanyar zuwa Horonayim suna makoki saboda hallakawarsu.
6 Porque las aguas de Nimrim quedarán desoladas; porque la hierba se ha marchitado, la hierba tierna se ha secado, no hay nada verde.
Ruwayen Nimrim sun ƙafe ciyayin kuma sun bushe; tsire-tsire duk sun ɓace babu sauran ɗanyen abu.
7 Por eso se llevarán la abundancia que han conseguido, y lo que han almacenado, sobre el arroyo de los sauces.
Saboda haka dukiyar da suka tara suka kuma ajiye sun ɗauka suka ƙetare Rafin Arabim da su.
8 Porque el clamor ha recorrido las fronteras de Moab, su lamento hasta Eglaim, y su lamento hasta Beer Elim.
Ƙugin kukansu ya kai ko’ina a iyakar Mowab; kururuwarsu ta kai har zuwa Eglayim, makokinsu ya kai har zuwa Beyer-Elim.
9 Porque las aguas de Dimón están llenas de sangre; porque aún traeré más sobre Dimón, un león sobre los de Moab que escapan, y sobre el resto de la tierra.
Ruwayen Dimon sun cika da jini, amma zan yi ƙari a kan Dimon, zan kawo zaki a kan masu gudu na Mowab da kuma a kan waɗanda suka ragu a ƙasar.

< Isaías 15 >