< Génesis 7 >
1 Yahvé dijo a Noé: “Sube con toda tu familia a la nave, porque he visto tu justicia ante mí en esta generación.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Nuhu. “Shiga jirgin, kai da dukan iyalinka, gama na ga kai mai adalci ne a wannan zamani.
2 Llevarás contigo siete parejas de cada animal limpio, el macho y su hembra. De los animales que no están limpios, toma dos, el macho y su hembra.
Ka ɗauki bakwai na kowace iri tsabtaccen dabba tare da kai, namiji da ta mace, da kuma biyu na kowace dabba marar tsabta, namiji da ta mace,
3 También de las aves del cielo, siete y siete, macho y hembra, para mantener viva la semilla en la superficie de toda la tierra.
da kuma bakwai na kowane iri tsuntsu, namiji da ta mace, domin a bar kowane irinsu da rai a dukan duniya.
4 En siete días haré llover sobre la tierra durante cuarenta días y cuarenta noches. Destruiré todo ser viviente que he hecho de la superficie de la tierra”.
Kwana bakwai daga yanzu zan aiko da ruwa a duniya yini arba’in da dare arba’in, zan kuma kawar da kowace halitta mai rai da na yi daga doron ƙasa.”
5 Noé hizo todo lo que Yahvé le ordenó.
Nuhu ya aikata duk abin da Ubangiji ya umarce shi.
6 Noé tenía seiscientos años cuando el diluvio de aguas llegó a la tierra.
Nuhu yana da shekaru 106 ne sa’ad da aka yi ambaliya ruwa a duniya.
7 Noé subió a la nave con sus hijos, su mujer y las mujeres de sus hijos, a causa de las aguas del diluvio.
Nuhu da matarsa da’ya’yansa da matansu, suka shiga jirgi domin su tsira daga ruwa ambaliya.
8 Los animales limpios, los inmundos, las aves y todo lo que se arrastra por el suelo
Biyu-biyu daga dabbobi masu tsabta da marasa tsabta, da tsuntsaye da kuma dukan halittu masu rarrafe a ƙasa,
9 entraron por parejas con Noé en la nave, machos y hembras, como Dios le había ordenado a Noé.
namiji da ta mace, suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi, kamar yadda Allah ya umarce Nuhu.
10 Después de los siete días, las aguas de la inundación llegaron a la tierra.
Bayan kwana bakwai kuwa ambaliya ruwa ta sauko a bisa duniya.
11 En el año seiscientos de la vida de Noé, en el segundo mes, a los diecisiete días del mes, ese día estallaron todas las fuentes del gran abismo y se abrieron las ventanas del cielo.
A ranar sha bakwai ga wata na biyu, na shekara ta ɗari shida na rayuwar Nuhu, a ran nan sai dukan maɓuɓɓugai na manyan zurfafa suka fashe, tagogin sammai suka buɗe.
12 Llovió sobre la tierra durante cuarenta días y cuarenta noches.
Ruwa yana ta kwararowa bisa duniya, yini arba’in da dare arba’in.
13 En el mismo día Noé, y Sem, Cam y Jafet — los hijos de Noé — y la esposa de Noé y las tres esposas de sus hijos con ellos, entraron en la nave —
A wannan rana Nuhu tare da matarsa da’ya’yansa maza, Shem, Ham da Yafet da matansu uku suka shiga jirgi.
14 ellos, y todo animal según su especie, todo el ganado según su especie, todo reptil que se arrastra sobre la tierra según su especie, y toda ave según su especie, toda ave de toda clase.
Tare da su kuwa, akwai kowane naman jeji bisa ga irinsa, da dukan dabbobin gida bisa ga irinsu, da kowace halitta mai rarrafe a ƙasa bisa ga irinta, da kowane tsuntsun gida da na jeji bisa ga irinsa, da dukan abu mai fiffike.
15 Las parejas de toda carne con aliento de vida entraron en la nave hacia Noé.
Biyu-biyu na dukan halittu masu numfashi suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi.
16 Los que entraron, entraron macho y hembra de toda carne, como Dios le ordenó; entonces Yahvé lo encerró.
Dabbobi da kowane abu mai rai da suka shiga ciki, namiji ne da ta mace, yadda Allah ya umarci Nuhu. Sa’an nan Ubangiji ya kulle jirgin daga baya.
17 El diluvio duró cuarenta días sobre la tierra. Las aguas aumentaron, y levantaron la nave, y ésta se elevó sobre la tierra.
Kwana arba’in ambaliya ta yi ta saukowa a duniya, sa’ad da ruwa ya yi ta ƙaruwa sai ya yi ta ɗaga jirgin sama, ya kuwa tashi can bisa duniya.
18 Las aguas crecieron y aumentaron mucho sobre la tierra, y el barco flotaba sobre la superficie de las aguas.
Ruwa ya taso, ya ƙaru ƙwarai a duniya, jirgin kuma ya yi ta yawo a bisa ruwa.
19 Las aguas se elevaron mucho sobre la tierra. Todos los montes altos que había bajo todo el cielo quedaron cubiertos.
Ruwa ya ƙaru ƙwarai a duniya, ya kuma rufe dukan duwatsu masu tsawo a ƙarƙashin sammai.
20 Las aguas subieron quince codos más, y las montañas quedaron cubiertas.
Ruwan ya taso ya rufe duwatsu, zurfin ruwa daga duwatsun zuwa inda jirgin yake ya fi ƙafa ashirin.
21 Murió toda la carne que se movía sobre la tierra, incluyendo las aves, el ganado, los animales, todo lo que se arrastra sobre la tierra y todo hombre.
Kowane abu mai rai da yake tafiya a duniya ya hallaka, tsuntsaye, dabbobin gida, namun jeji, da dukan masu rarrafe waɗanda suke rarrafe a duniya, da kuma dukan mutane.
22 Murió todo lo que estaba en la tierra firme, en cuyas narices había aliento de espíritu de vida.
Kome a busasshiyar ƙasa da yake numfashi a hancinsa ya mutu.
23 Fue destruido todo ser viviente que estaba sobre la superficie de la tierra, incluidos el hombre, el ganado, los reptiles y las aves del cielo. Fueron destruidos de la tierra. Sólo quedó Noé y los que estaban con él en la nave.
Aka kawar da kowane abu mai rai, mutane da dabbobi da halittu masu rarrafe a ƙasa, da tsuntsayen sama a doron ƙasa, duka aka kawar da su daga duniya. Nuhu kaɗai aka bari da waɗanda suke tare da shi a cikin jirgi.
24 Las aguas inundaron la tierra durante ciento cincuenta días.
Ruwa ya mamaye duniya har kwana ɗari da hamsin.