< Génesis 40 >

1 Después de estas cosas, el copero del rey de Egipto y su panadero ofendieron a su señor, el rey de Egipto.
Bayan ɗan lokaci, sai mai riƙon kwaf da mai tuyan sarkin Masar suka yi wa maigidansu, sarkin Masar laifi.
2 El faraón se enojó con sus dos oficiales, el jefe de los coperos y el jefe de los panaderos.
Fir’auna ya yi fushi da hafsoshin nan nasa guda biyu, shugaban masu shayarwa da shugaban masu tuya,
3 Los puso en custodia en la casa del capitán de la guardia, en la cárcel, el lugar donde estaba atado José.
ya kuma sa su a kurkuku a cikin gidan shugaban masu tsaro, a wannan kurkukun da aka sa Yusuf.
4 El capitán de la guardia se los asignó a José, y él se ocupó de ellos. Permanecieron en la cárcel muchos días.
Sai shugaban masu tsaro ya danƙa su a hannun Yusuf, ya kuwa yi musu hidima. Bayan sun jima cikin kurkuku,
5 Ambos soñaron un sueño, cada uno su sueño, en una noche, cada uno según la interpretación de su sueño, el copero y el panadero del rey de Egipto, que estaban atados en la cárcel.
sai kowanne a cikin mutum biyun nan, mai riƙon kwaf da mai tuya na sarkin Masar, waɗanda aka sa a kurkuku, suka yi mafarki a dare ɗaya, kuma kowane mafarki ya kasance da fassara irin tasa.
6 José entró a ellos por la mañana, los vio y vio que estaban tristes.
Sa’ad da Yusuf ya zo wurinsu kashegari, sai ya ga duk sun damu.
7 Preguntó a los oficiales del faraón que estaban con él detenidos en la casa de su amo, diciendo: “¿Por qué parecen tan tristes hoy?”
Saboda haka ya tambayi hafsoshin Fir’auna, waɗanda suke a kurkuku tare da shi, a gidan maigidansa ya ce, “Me ya sa fuskokinku suke a ɓace haka?”
8 Le dijeron: “Hemos soñado un sueño y no hay nadie que pueda interpretarlo”. José les dijo: “¿Las interpretaciones no son de Dios? Por favor, díganmelo a mí”.
Sai suka amsa, “Mu biyu, mun yi mafarki, amma babu wani da zai fassara mana su.” Sa’an nan Yusuf ya ce musu, “Fassara ba daga Allah take zuwa ba? Ku faɗa mini mafarkanku.”
9 El jefe de los coperos contó su sueño a José y le dijo: “En mi sueño, he aquí que una vid estaba delante de mí,
Sai shugaban masu shayarwa ya faɗa wa Yusuf mafarkinsa. Ya ce masa, “A cikin mafarkina, na ga kuringa a gabana,
10 y en la vid había tres sarmientos. Era como si hubiera brotado, florecido, y sus racimos producían uvas maduras.
kuma a kuringar, akwai rassa uku. Nan da nan kuringar ta yi toho, ta huda, ta kuma yi nonna har suka nuna, suka zama inabi.
11 La copa del faraón estaba en mi mano; tomé las uvas, las exprimí en la copa del faraón y entregué la copa en la mano del faraón.”
Kwaf Fir’auna kuwa yana a hannuna, na kuma ɗiba inabin na matse su cikin kwaf Fir’auna, na kuma sa kwaf ɗin a hannunsa.”
12 José le dijo: “Esta es su interpretación: las tres ramas son tres días.
Yusuf ya ce masa, “Ga abin da mafarkin yake nufi, ‘Rassan nan uku, kwana uku ne.
13 Dentro de tres días más, el faraón levantará tu cabeza y te devolverá tu cargo. Entregarás la copa del Faraón en su mano, como lo hacías cuando eras su copero.
Cikin kwana uku, Fir’auna zai fitar da kai, yă maido da kai a matsayinka, za ka kuwa sa kwaf Fir’auna cikin hannunsa, kamar yadda ka saba yi sa’ad da kake mai riƙon kwaf nasa.
14 Pero acuérdate de mí cuando te vaya bien. Por favor, muéstrate bondadoso conmigo, y mencióname ante el Faraón, y sácame de esta casa.
Amma fa, sa’ad da kome ya zama maka da kyau, ka tuna da ni, ka kuma yi mini alheri, ka ambace ni wa Fir’auna, ka fid da ni daga wannan kurkuku.
15 Porque ciertamente fui robado de la tierra de los hebreos, y aquí tampoco he hecho nada para que me metan en el calabozo.”
Gama da ƙarfi ne aka ɗauke ni daga ƙasar Ibraniyawa, ko a nan ma ban yi wani abin da ya cancanci a sa ni cikin kurkuku ba.’”
16 Cuando el jefe de los panaderos vio que la interpretación era buena, dijo a José: “Yo también estaba en mi sueño, y he aquí que tres cestas de pan blanco estaban sobre mi cabeza.
Sa’ad da shugaban masu tuya ya ga cewa Yusuf ya ba da fassara mai gamsarwa, sai ya ce, wa Yusuf, “Ni ma na yi mafarki. A kaina, akwai kwanduna uku na burodi.
17 En el cesto de arriba había toda clase de alimentos horneados para el Faraón, y las aves los comían del cesto sobre mi cabeza.”
A kwandon na bisa, akwai kayan iri-iri da aka toya, masu kyau domin Fir’auna, amma tsuntsaye suka ci su a kwandon da yake kaina.”
18 José respondió: “Esta es su interpretación. Los tres cestos son tres días.
Yusuf ya ce, “Ga abin da mafarkin yake nufi, ‘Kwanduna uku, kwanaki uku ne.
19 Dentro de tres días más, el Faraón levantará tu cabeza de encima, te colgará en un árbol y las aves comerán tu carne de encima.”
Cikin kwana uku, Fir’auna zai fid da kai, yă rataye ka a kan itace. Tsuntsaye kuwa za su ci naman jikinka.’”
20 Al tercer día, que era el cumpleaños del Faraón, éste hizo un banquete para todos sus servidores, y levantó la cabeza del jefe de los coperos y la del jefe de los panaderos entre sus servidores.
To, a rana ta uku ne, ranar tunawa da haihuwar Fir’auna, ya kuwa yi biki wa dukan hafsoshinsa. Ya fid da shugaban masu shayarwa da kuma shugaban masu tuya a gaban hafsoshinsa.
21 Restituyó al jefe de los coperos a su puesto, y entregó la copa a la mano del Faraón;
Ya mai da shugaban masu shayarwa a matsayinsa, saboda haka shugaban masu shayarwa ya sāke sa kwaf a hannun Fir’auna,
22 pero colgó al jefe de los panaderos, como José les había interpretado.
amma ya rataye shugaban masu tuya, kamar dai yadda Yusuf ya faɗa musu a fassarar mafarkan da suka yi.
23 Sin embargo, el jefe de los coperos no se acordó de José, sino que lo olvidó.
Shugaban masu shayarwa fa, bai tuna da Yusuf ba; ya mance da shi.

< Génesis 40 >