< Ezequiel 23 >

1 La palabra de Yahvé vino de nuevo a mí, diciendo:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “Hijo de hombre, había dos mujeres, hijas de una misma madre.
“Ɗan mutum, an yi mata biyu,’yan matan mahaifiya guda.
3 Hicieron de prostituta en Egipto. Jugaron a la prostitución en su juventud. Allí les acariciaban los pechos y les acariciaban los pezones en su juventud.
Suka zama karuwai a Masar, suka yi karuwanci tun daga ƙuruciyarsu. A wancan ƙasar an rungumi mamansu da ƙirjinsu na budurwanci.
4 Sus nombres eran Oholah la mayor y Oholibah su hermana. Se hicieron mías, y dieron a luz hijos e hijas. En cuanto a sus nombres, Samaria es Oholah, y Jerusalén Oholibah.
Sunan babbar Ohola, ƙanuwarta kuwa Oholiba. Sun zama nawa suka kuma haifi’ya’ya maza da mata. Ohola ita ce Samariya, Oholiba kuwa ita ce Urushalima.
5 “Oholah jugaba a la prostitución cuando era mía. Ella se prostituía con sus amantes, con los asirios sus vecinos,
“Ohola ta shiga karuwanci yayinda take zamana; ta kuwa yi ta kai da kawowa da kwartayenta, Assuriyawa, mayaƙa
6 que estaban vestidos de azul-gobernantes y gobernantes, todos ellos jóvenes deseables, jinetes montados a caballo.
waɗanda suke saye da shunayya, gwamnoni da manyan sojoji, dukansu samari ne masu bansha’awa, suna bisa kan dawakai.
7 Se entregó a ellos como prostituta, a todos los hombres más selectos de Asiria. Se profanó con los ídolos de quienquiera que deseara.
Ta ba da kanta ga duk waɗanda suke masu ilimin Assuriya ta kuma ƙazantar da kanta da dukan gumaka na kowa da take kai da kawowa a cikinsu.
8 No dejó su prostitución desde que salió de Egipto, pues en su juventud se acostaron con ella. Acariciaron sus pezones juveniles y derramaron sobre ella su prostitución.
Ba ta bar karuwancin da ta fara a Masar ba, sa’ad da take budurwa maza sun kwana da ita, suka rungumi ƙirjinta suka kuma biya kwaɗayinsu a kanta.
9 “Por eso la entregué en manos de sus amantes, en manos de los asirios a los que se dedicaba.
“Saboda haka na bashe ta ga kwartayenta, Assuriyawa, waɗanda ta yi ta kai da kawowa a cikinsu.
10 Estos descubrieron su desnudez. Tomaron a sus hijos y a sus hijas, y la mataron a espada. Se convirtió en un sinónimo entre las mujeres, pues ejecutaron juicios contra ella.
Suka tuɓe ta tsirara, suka kwashe’ya’yanta maza da mata suka kuma kashe ta da takobi. Ta kuwa zama abin karin magana a cikin mata, aka kuma yi mata hukunci.
11 “Su hermana Oholibah lo vio, pero se corrompió más que ella en su lujuria y en su prostitución, que era más depravada que la de su hermana.
“Ƙanuwarta Oholiba kuwa ta ga wannan, duk da haka cikin kai da kawowarta da karuwancinta ta fi’yar’uwar lalacewa.
12 Ella codiciaba a los asirios, a los gobernadores y a los gobernantes, a sus vecinos, vestidos de la manera más hermosa, a los jinetes que montaban a caballo, todos ellos jóvenes deseables.
Ita ma ta yi ta kai da kawowa cikin Assuriyawa, gwamnoni da manyan sojoji; mayaƙa masu saye da kayan yaƙi, suna bisa dawakai, dukansu samari ne masu bansha’awa.
13 Vi que se había contaminado. Las dos iban por el mismo camino.
Na ga cewa ita ma ta ƙazantar da kanta; dukansu biyu sun bi hanya guda.
14 “Aumentó su prostitución, porque vio a hombres retratados en la pared, las imágenes de los caldeos retratados con rojo,
“Amma karuwancinta ya zarce. Ta ga an zāna mutane a kan bango, siffofin sojojin Kaldiyawa suna cikin jajjayen riguna,
15 vestidos con cinturones en la cintura, con turbantes fluidos en la cabeza, todos ellos con aspecto de príncipes, a semejanza de los babilonios en Caldea, la tierra de su nacimiento.
da ɗamara a gindinsu da rawuna a kansu suna kaɗawa falfal; dukansu sun yi kamar jarumawan kekunan yaƙin Babiloniyawa’yan Kaldiya.
16 En cuanto los vio, los codició y les envió mensajeros a Caldea.
Nan da nan da ta gan su, sai ta yi sha’awarsu ta aika da’yan aika zuwa wurinsu a Kaldiya.
17 Los babilonios se acercaron a ella en el lecho del amor, y la profanaron con su prostitución. Se contaminó con ellos, y su alma se alejó de ellos.
Sai Babiloniyawan suka zo wurinta, zuwa gadon soyayya, cikin kai da kawowarsu suka ƙazantar da ita. Bayan sun ƙazantar da ita, sai ta ji ƙyamarsu, ta rabu da su.
18 Entonces ella descubrió su prostitución y descubrió su desnudez. Entonces mi alma se alejó de ella, como mi alma se alejó de su hermana.
Sa’ad da ta ci gaba da yin karuwancinta a fili ta kuma nuna tsiraicinta, sai na ji ƙyamarta, na rabu da ita, kamar dai yadda na rabu da’yar’uwarta.
19 Sin embargo, ella multiplicó su prostitución, recordando los días de su juventud, en los que había jugado a la prostitución en la tierra de Egipto.
Duk da haka sai ta yi ta ƙara fasikanci tana tuna da kwanakin budurcinta, sa’ad da take karuwa a Masar.
20 Codició a sus amantes, cuya carne es como la de los asnos, y cuyo flujo es como el de los caballos.
A can ta yi ta kai da kawowa da kwartayenta, waɗanda al’auransu kamar na jakuna ne waɗanda maniyyinsu kuwa kamar na dawakai ne.
21 Así llamaste a la memoria la lascivia de tu juventud, en la caricia de tus pezones por parte de los egipcios a causa de tus pechos juveniles.
Haka kika yi ta lalacin budurcinki, sa’ad da a Masar aka rungumi ƙirjinta aka tattaɓa nononta.
22 “Por eso, Oholibá, el Señor Yahvé dice: ‘He aquí que yo levanto contra ti a tus amantes, de los que tu alma está enajenada, y los traigo contra ti por todos lados:
“Saboda haka, Oholiba, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan zuga kwartayenki su yi gāba da ke, su waɗanda kika ji ƙyamarsu, zan kuma kawo su su yi gāba da ke daga kowane gefe,
23 los babilonios y todos los caldeos, Pekod, Shoa, Koa, y todos los asirios con ellos; todos ellos jóvenes deseables, gobernadores y gobernantas, príncipes y hombres de renombre, todos ellos montados a caballo.
Babiloniyawa da dukan Kaldiyawa, mutanen Fekod da Showa da Kowa, da dukan Assuriyawa, samari masu bansha’awa, dukan gwamnoni da manyan sojoji, hafsoshin keken yaƙin da mutane masu manyan matsayi, dukansu a bisa dawakai.
24 Vendrán contra ti con armas, carros y carretas, y con una compañía de pueblos. Se pondrán en contra de ti con escudo y casco alrededor. Les encomendaré el juicio, y ellos te juzgarán según sus juicios.
Za su yi gāba da ke da kayan yaƙi, kekunan yaƙi da kekunan doki da mutane masu yawa; za su ja dāgā a kanki a kowane gefe da garkuwoyi manya da ƙanana da kuma hulunan kwano. Zan miƙa ke gare su don hukunci, za su kuma hukunta ki bisa ga shari’arsu.
25 Pondré mi celo contra ti, y te tratarán con furia. Te quitarán la nariz y las orejas. Tu remanente caerá por la espada. Se llevarán a tus hijos y a tus hijas, y el resto de vosotros será devorado por el fuego.
Zan nuna fushin kishina a kanki, za su kuwa wulaƙanta ki da fushi. Za su yanke hancinki da kunnuwanki, waɗanda suka rage miki kuma za a kashe su da takobi. Za su kama’ya’yanki maza da mata, waɗanda suka rage miki kuwa za a ƙone su da wuta.
26 También te despojarán de tus ropas y te quitarán tus hermosas joyas.
Za su tuɓe tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau.
27 Así haré que cese de vosotros vuestra lascivia, y quitaré vuestra prostitución de la tierra de Egipto, para que no levantéis vuestros ojos hacia ellos, ni os acordéis más de Egipto.’
Ta haka zan tsai da marmari da kuma karuwancin da kika fara a Masar. Ba za ki dubi waɗannan abubuwa da marmari ko ki ƙara tuna da Masar ba.
28 “Porque el Señor Yahvé dice: ‘He aquí que yo te entregaré en mano de aquellos a quienes odias, en mano de aquellos de quienes tu alma está enajenada.
“Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina shirin miƙa ki ga waɗanda suke ƙinki, ga waɗanda kika ji ƙyamarsu kika rabu da su.
29 Ellos te tratarán con odio, y te quitarán todo tu trabajo, y te dejarán desnuda y descubierta. La desnudez de tu prostitución será descubierta, tanto tu lascivia como tu prostitución.
Za su hukunta ki da ƙiyayya su kuma kwashe kome da kika yi wahalarsa. Za su bar ki tsirara tik, kunyan karuwancinki kuma zai tonu. Marmarinki da fasikancinki
30 Estas cosas te sucederán porque te has prostituido según las naciones, y porque te has contaminado con sus ídolos.
sun jawo miki wannan, domin ki yi ta kai da kawowa cikin ƙasashe kina ƙazantar da kanki da gumakansu.
31 Has seguido el camino de tu hermana; por eso entregaré su copa en tu mano’.
Kin bi hanyar’yar’uwarki; saboda haka zan sa kwaf nata a hannunki.
32 “El Señor Yahvé dice: ‘Beberás de la copa de tu hermana, que es profundo y grande. Se le ridiculizará y se le ridiculizará. Contiene mucho.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Za ki sha kwaf na’yar’uwarki, kwaf wanda yake da girma da kuma zurfi; zai jawo dariya da kuma reni gama yana ɗauke da abubuwa da yawa.
33 Te llenarás de embriaguez y de tristeza, con la copa del asombro y la desolación, con la copa de tu hermana Samaria.
Za ki cika da buguwa da baƙin ciki, kwaf lalaci da kaɗaici, kwaf na’yar’uwarki Samariya.
34 Incluso lo beberás y lo escurrirás. Roerás los trozos rotos, y desgarrará tus pechos; porque yo lo he dicho’, dice el Señor Yahvé.
Za ki sha shi ki kuma lashe shi ƙaf; za ki buga shi da ƙasa ya yi rugu-rugu ki tsattsage nononki. Ni Ubangiji Mai Iko Duka na faɗa.
35 “Por eso dice el Señor Yahvé: ‘Como me has olvidado y me has echado a tus espaldas, por eso también soportas tu lascivia y tu prostitución’”.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa da yake kin manta da ni kika tura ni bayanki, dole ki sha sakamakon marmarinki da karuwancinki.”
36 El Señor me dijo además: “Hijo de hombre, ¿vas a juzgar a Oholah y a Oholibah? Entonces declárales sus abominaciones.
Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, za ka shari’anta Ohola da Oholiba? To, sai ka kalubalance su da ayyukansu masu banƙyama,
37 Porque han cometido adulterio, y hay sangre en sus manos. Han cometido adulterio con sus ídolos. También han hecho pasar por el fuego a sus hijos que me han dado a luz, para que sean devorados.
gama sun yi zina kuma jinin yana a hannuwansu. Sun yi zina da gumakansu; har suka miƙa’ya’yansu da suka haifa mini, su zama musu abinci.
38 Además, esto me han hecho: han profanado mi santuario en el mismo día, y han profanado mis sábados.
Sun kuma yi mini wannan. A lokaci guda sun ƙazantar da wuri mai tsarkina suka ɓata Asabbataina.
39 Porque cuando mataron a sus hijos para sus ídolos, vinieron el mismo día a mi santuario para profanarlo; y he aquí que han hecho esto en medio de mi casa.
A ranar da suka miƙa’ya’yansu ga gumakansu, sai suka shiga wuri mai tsarkina suka kuma ƙazantar da shi. Abin da suka yi a gidana ke nan.
40 “Además, vosotras, hermanas, habéis mandado llamar a unos hombres que vienen de lejos, a los que se envió un mensajero, y he aquí que vinieron; para los que os lavasteis, os pintasteis los ojos, os adornasteis con ornamentos,
“Sun ma aiki manzanni wa mutanen da suka zo daga nesa, kuma da suka iso kun yi wanka dominsu, kuka yi shafe-shafen idanunku, kuka kuma sa kayan adonku.
41 y os sentasteis en un lecho majestuoso, con una mesa preparada delante, en la que pusisteis mi incienso y mi aceite.
Kuka zauna a gado mai daraja, da tebur a shirye a gabanku wanda kun ajiye turare da maina.
42 “La voz de una multitud que estaba a gusto estaba con ella. Con los hombres de la plebe fueron traídos borrachos del desierto; y se pusieron brazaletes en las manos, y hermosas coronas en la cabeza.
“Surutun taron mutane marasa kula suna kewaye da ita; aka kawo Sabenawa daga hamada tare da mutane daga mashaya, suka sa mundaye a hannuwan macen da kuma’yar’uwarta suka kuma sa rawani masu kyau a kawunansu.
43 Entonces dije de la que era vieja en adulterios: ‘Ahora jugarán a la prostitución con ella, y ella con ellos’.
Sai na yi magana a kan wadda ta ƙare ƙarfi ta wurin karuwanci na ce, ‘Yanzu bari su yi amfani da ita kamar karuwa, gama abin da take ke nan.’
44 Entraron a ella, como se entra a una prostituta. Así entraron a Oholah y a Oholibah, las mujeres lascivas.
Suka kuwa kwana da ita. Kamar yadda maza suke kwana ta karuwa, haka suka kwana da waɗannan lalatattun mata, Ohola da Oholiba.
45 Los hombres justos las juzgarán con el juicio de las adúlteras y con el juicio de las mujeres que derraman sangre, porque son adúlteras y tienen sangre en sus manos.
Amma masu adalci za su hukunta su irin da akan yi wa matan da suka yi zina suka kuma yi kisa, domin su mazinata ne kuma jini yana a hannuwansu.
46 “Porque el Señor Yahvé dice: ‘Traeré una turba contra ellos, y los daré para que los arrojen de un lado a otro y los roben.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kawo taron mutane a kansu a kuma miƙa su don a firgitar da su a kuma washe su.
47 La turba los apedreará y los despachará con sus espadas. Matarán a sus hijos y a sus hijas, y quemarán sus casas con fuego.
Taron mutanen za su jajjefe su, su kuma sassare su da takuba; za su kashe’ya’yansu maza da mata su kuma ƙone gidajensu.
48 “‘Así haré cesar la lascivia de la tierra, para que todas las mujeres sean enseñadas a no ser lascivas como tú.
“Ta haka zan kawo ƙarshe ga lalaci a ƙasar, don dukan mata su ji gargaɗi kada kuma su kwaikwaye ku
49 Ellos pagarán su lascivia sobre ustedes, y cargarán con los pecados de sus ídolos. Entonces sabrás que yo soy el Señor Yahvé’”.
Za ku sha hukuncin lalacinku ku kuma ɗauki hakkin zunuban bautar gumaka. Sa’an nan za ku san cewa Ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ezequiel 23 >