< Éxodo 7 >
1 Yahvé dijo a Moisés: “He aquí que te he puesto como Dios ante el Faraón, y Aarón tu hermano será tu profeta.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Duba, na maishe ka kamar Allah ga Fir’auna, ɗan’uwanka Haruna kuma zai zama annabinka.
2 Tú hablarás todo lo que yo te mande; y Aarón tu hermano hablará al Faraón para que deje salir a los hijos de Israel de su tierra.
Za ka faɗi kome da na umarce ka, ɗan’uwanka Haruna kuwa zai faɗa wa Fir’auna, yă bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa.
3 Yo endureceré el corazón del Faraón, y multiplicaré mis señales y mis prodigios en la tierra de Egipto.
Amma zan taurare zuciyar Fir’auna, kuma ko da na ninka mu’ujizai da kuma alamu a Masar,
4 Pero el Faraón no te escuchará, así que pondré mi mano sobre Egipto y sacaré a mis ejércitos, a mi pueblo los hijos de Israel, de la tierra de Egipto con grandes juicios.
ba zai saurare ku ba. Don haka zan miƙa hannuna a kan Masar, in murƙushe ta da bala’i iri-iri, bayan haka zan fitar da taron mutanen Isra’ila daga ƙasar Masar ta wurin hukuntaina masu girma.
5 Los egipcios sabrán que yo soy Yahvé cuando extienda mi mano sobre Egipto y saque a los hijos de Israel de entre ellos.”
Masarawa kuwa za su san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na miƙa hannuna a kan Masar, na kuma fitar da Isra’ilawa daga gare ta.”
6 Moisés y Aarón lo hicieron. Como el Señor les ordenó, así lo hicieron.
Musa da Haruna suka aikata yadda Ubangiji ya umarce su.
7 Moisés tenía ochenta años, y Aarón ochenta y tres, cuando hablaron con el faraón.
Musa yana da shekara tamanin da haihuwa, Haruna kuma yana da shekara tamanin da uku, sa’ad da suka yi magana da Fir’auna.
8 Yahvé habló a Moisés y a Aarón, diciendo:
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
9 “Cuando el Faraón les hable diciendo: ‘Hagan un milagro’, entonces le dirán a Aarón: ‘Toma tu vara y arrójala ante el Faraón, y se convertirá en una serpiente’”.
“Sa’ad da Fir’auna ya ce muku, ‘Aikata wani al’ajabi,’ sai ka ce wa Haruna, ‘Ɗauki sandanka ka jefa shi a ƙasa, a gaban Fir’auna,’ zai kuwa zama maciji.”
10 Moisés y Aarón se presentaron ante el faraón, y así lo hicieron, tal como lo había ordenado el Señor. Aarón arrojó su vara ante el Faraón y ante sus servidores, y se convirtió en una serpiente.
Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna, suka yi yadda Ubangiji ya umarce su. Haruna ya jefa sandansa ƙasa, a gaban Fir’auna da bayinsa, sai sandan ya zama maciji.
11 Entonces el faraón llamó también a los sabios y a los hechiceros. Ellos también, los magos de Egipto, hicieron lo mismo con sus encantamientos.
Fir’auna kuwa ya kira masu hikima da masu sihiri, sai bokayen Masarawa ma suka yi irin abubuwan nan da bokancinsu.
12 Cada uno de ellos arrojó su vara y se convirtió en serpiente; pero la vara de Aarón se tragó sus varas.
Kowannensu ya jefa sandansa ƙasa, ya kuwa zama maciji. Amma sandan Haruna ya haɗiye sandunansu.
13 El corazón del faraón se endureció y no los escuchó, como había dicho el Señor.
Duk da haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurare su ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
14 El Señor dijo a Moisés: “El corazón del faraón es obstinado. Se niega a dejar ir al pueblo.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Zuciyar Fir’auna taurariya ce, ya ƙi yă bar mutanen su tafi.
15 Ve a ver al faraón por la mañana. He aquí que él va a salir al agua. Tú estarás a la orilla del río para recibirlo. Tomarás en tu mano la vara convertida en serpiente.
Ka je wurin Fir’auna da safe, yayinda za shi kogi. Ka jira a bakin Nilu don ka sadu da shi, ka ɗauki sandan nan da ya canja zuwa maciji a hannunka.
16 Le dirás: “Yahvé, el Dios de los hebreos, me ha enviado a ti, diciendo: “Deja ir a mi pueblo, para que me sirva en el desierto. He aquí que hasta ahora no has hecho caso”.
Sa’an nan ka ce masa, ‘Ubangiji, Allah na Ibraniyawa, ya aiko ni in faɗa maka, Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada a hamada. Amma har yanzu ba ka yi biyayya ba.
17 Yahvé dice: “En esto sabrán que yo soy Yahvé. Miren: Golpearé con la vara que tengo en mi mano las aguas que están en el río, y se convertirán en sangre.
Ga abin da Ubangiji ya ce, da wannan za ka san cewa ni ne Ubangiji. Da sandan da yake hannuna zan bugi ruwan Nilu, zai kuma zama jini.
18 Los peces que están en el río morirán y el río se ensuciará. Los egipcios detestarán beber agua del río”.
Kifi a ciki Nilu za su mutu, ruwan kuma zai yi ɗoyi; Masarawa ba za su iya shan ruwansa ba.’”
19 Yahvé dijo a Moisés: “Dile a Aarón: ‘Toma tu vara y extiende tu mano sobre las aguas de Egipto, sobre sus ríos, sobre sus arroyos y sobre sus estanques, y sobre todos sus estanques de agua, para que se conviertan en sangre. Habrá sangre en toda la tierra de Egipto, tanto en los recipientes de madera como en los de piedra’”.
Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka ɗauki sandanka, ka miƙa hannunka kan ruwan Masar, kan kogunansu da rafuffukansu da kududdufansu da kuma dukan tafkunansu, za su zama jini.’ Jini zai kasance ko’ina a Masar, har ma a cikin abubuwan ajiyar ruwansu da aka yi da itace da kuma dutse.”
20 Moisés y Aarón lo hicieron así, tal como lo había ordenado el Señor, y él levantó la vara y golpeó las aguas que estaban en el río, a la vista del Faraón y de sus servidores, y todas las aguas que estaban en el río se convirtieron en sangre.
Musa da Haruna suka yi yadda Ubangiji ya umarta. Ya ɗaga sandansa a gaban Fir’auna da bayinsa, ya bugi ruwan Nilu, dukan ruwan kuwa ya zama jini.
21 Los peces que había en el río murieron. El río se volvió fétido. Los egipcios no podían beber agua del río. La sangre se extendió por toda la tierra de Egipto.
Kifin da suke cikin Nilu suka mutu, kogin kuwa ya yi wari sosai yadda Masarawa ba su iya shan ruwan ba. Jini ya bazu ko’ina a Masar.
22 Los magos de Egipto hicieron lo mismo con sus encantamientos. Así que el corazón del faraón se endureció y no les hizo caso, como había dicho el Señor.
Amma bokayen Masar ma suka yi abubuwan nan da sihirinsu, sai zuciyar Fir’auna ta taurare; bai saurari Musa da Haruna ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
23 El faraón se volvió y entró en su casa, y ni siquiera lo tomó en cuenta.
A maimakon yă saurara, sai ya juya ya koma fadarsa, bai ma damu da abin da aka yi ba.
24 Todos los egipcios cavaron alrededor del río en busca de agua para beber, porque no podían beber el agua del río.
Sai dukan Masarawa suka yi ta tonon gefen Nilu don su sami ruwan sha, domin ba su iya shan ruwan kogin ba.
25 Se cumplieron siete días, después de que el Señor golpeó el río.
Kwana bakwai suka wuce bayan da Ubangiji ya bugi kogin.