< Éxodo 23 >
1 “No difundirás una noticia falsa. No juntes tu mano con la del malvado para ser un testigo malicioso.
“Kada ku baza rahoton ƙarya. Kada kuma ku haɗa baki da mugayen mutane har da ku zama munafukai ta wurin ba da shaidar ƙarya.
2 “No seguirás a una multitud para hacer el mal. No testificarás en la corte para ponerte del lado de una multitud para pervertir la justicia.
“Kada ku yi abin da ba daidai ba, don galibin mutane suna yin haka. Sa’ad da kuke ba da shaida a gaban shari’a, kada ku ba da shaidar ƙarya a kauce wa gaskiya don ku faranta wa taron jama’a rai.
3 No favorecerás al pobre en su causa.
Kada ku yi wa matalauci sonkai a gaban shari’a.
4 “Si encuentras al buey de tu enemigo o a su asno extraviado, lo harás volver a él.
“In ka ga saniyar abokin gābanka, ko jakinsa ya ɓace, ka yi ƙoƙari ka mai da shi wurinsa.
5 Si ves que el asno del que te odia se ha caído bajo su carga, no lo dejes. Lo ayudarás con toda seguridad.
In ka ga jakin wani maƙiyinka ya fāɗi a ƙarƙashin kayan da ya ɗauka, kada ka bar shi can, ka yi ƙoƙari ka taimake shi.
6 “No negarás la justicia a tu pueblo pobre en sus pleitos.
“Kada ku kāsa yin adalci ga matalauci a wurin shari’a.
7 “Aléjate de una acusación falsa y no mates al inocente y al justo, porque no justificaré al impío.
Ku yi nesa da ƙage. Kada ku kashe marar laifi tare da mai adalci, gama ba zan bar mugun yă tafi haka kawai ba.
8 “No aceptarás soborno, porque el soborno ciega a los que tienen vista y pervierte las palabras de los justos.
“Kada ka karɓi cin hanci, gama cin hanci yakan makanta waɗanda suke gani, yakan kuma karkatar da maganar masu adalci.
9 “No oprimirás al extranjero, pues conoces el corazón del extranjero, ya que fuisteis extranjeros en la tierra de Egipto.
“Kada ka zalunci baƙo, ku kanku kun san halin baƙunci, gama dā ku baƙi ne a Masar.
10 “Durante seis años sembrarás tu tierra y recogerás sus frutos,
“Shekara shida za ku nome gonakinku ku girbe amfanin gonar,
11 pero el séptimo año la dejarás descansar y en barbecho, para que coman los pobres de tu pueblo; y lo que dejen lo comerá el animal del campo. Del mismo modo, te ocuparás de tu viña y de tu olivar.
amma a shekara ta bakwai za ku bar ƙasa tă huta. Sa’an nan matalautan da suke cikinku za su sami abinci daga cikinta, namun jeji kuma za su ci abin da aka bari. Ku yi haka da gonakinku na inabi, da na itatuwan zaitun.
12 “Seis días harás tu trabajo, y el séptimo día descansarás, para que tu buey y tu asno tengan descanso, y el hijo de tu siervo y el extranjero se refresquen.
“Kwana shida za ku yi aikinku, amma a rana ta bakwai, kada ku yi aiki, saboda saniyarku da jakinku su huta, haka kuma bawan da aka haifa a gidanku, da kuma baƙon da yake a cikinku yă wartsake.
13 “Cuida de hacer todo lo que te he dicho; y no invoques el nombre de otros dioses ni dejes que se oiga de tu boca.
“Ku mai da hankali, ku yi biyayya da duk abin da na faɗa muku. Kada ku kira sunaye waɗansu alloli; kada a ji su a bakinku.
14 “Celebrarás una fiesta para mí tres veces al año.
“Sau uku a shekara za ku yi mini biki.
15 Celebrarás la fiesta de los panes sin levadura. Siete días comeréis panes sin levadura, como os he mandado, en el tiempo señalado en el mes de Abib (porque en él salisteis de Egipto), y nadie se presentará vacío ante mí.
“Ku yi Bikin Burodi Marar Yisti, kwana bakwai za ku ci burodi marar yisti, kamar yadda na umarce ku. Ku yi wannan a lokacin da aka ayana a watan Abib, gama a watan ne kuka fito daga Masar. “Kada wani yă zo a gabana hannu wofi.
16 Y la fiesta de la cosecha, con los primeros frutos de vuestras labores, que sembréis en el campo; y la fiesta de la recolección, al final del año, cuando recojáis vuestras labores del campo.
“Ku yi Bikin Girbi da nunan fari na amfanin shuke-shuken gonarku. “Ku yi Bikin Tattarawa a ƙarshen shekara, sa’ad da kuka tattara amfani daga gonarku.
17 Tres veces al año se presentarán todos vuestros varones ante el Señor Yahvé.
“Sau uku a shekara, maza duka za su bayyana a gaban Ubangiji Mai Iko Duka.
18 “No ofrecerás la sangre de mi sacrificio con pan leudado. La grasa de mi fiesta no permanecerá toda la noche hasta la mañana.
“Kada ku miƙa mini hadayar jini tare da wani abu mai yisti. “Ba za a bar kitsen bikin hadayata yă kwana ba.
19 Traerás las primicias de tu tierra a la casa de Yahvé, tu Dios. “No hervirás un cabrito en la leche de su madre.
“Dole ne ku kawo mafi kyau daga nunan fari na gonakinku a gidan Ubangiji Allahnku. “Kada ku dafa ɗan akuya a cikin madarar mahaifiyarsa.
20 “He aquí que yo envío un ángel delante de ti, para que te guarde en el camino y te lleve al lugar que he preparado.
“Ga shi, zan aika mala’ika a gabanku, yă tsare ku a tafiyarku, yă kuma kawo ku wurin da na shirya.
21 Presta atención a él y escucha su voz. No lo provoques, porque no perdonará tu desobediencia, pues mi nombre está en él.
Ku saurare shi, ku kuma kasa kunne ga abin da yake faɗa. Kada ku yi masa tawaye; ba zai gafarta tawayenku ba, gama shi wakilina ne.
22 Pero si en verdad escuchas su voz y haces todo lo que yo digo, seré enemigo de tus enemigos y adversario de tus adversarios.
In kun kasa kunne sosai ga abin da yake faɗi, kuka kuma yi abin da na faɗa, zan zama magabci ga abokan gābanku, zan kuma yi hamayya da abokan hamayyanku.
23 Porque mi ángel irá delante de ti y te llevará ante el amorreo, el hitita, el ferezeo, el cananeo, el heveo y el jebuseo, y los eliminaré.
Mala’ikana zai sha gabanku, yă kawo ku cikin ƙasar Amoriyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Kan’aniyawa, da Hiwiyawa, da kuma Yebusiyawa, zan kuma kawar da su.
24 No te inclinarás ante sus dioses, ni los servirás, ni seguirás sus prácticas, sino que los derrocarás por completo y demolerás sus pilares.
Kada ku durƙusa wa allolinsu, ko ku yi musu sujada, ko kuma ku bi al’adunsu. Za ku hallaka dukan allolinsu, ku kuma farfasa keɓaɓɓun duwatsunsu.
25 Servirás a Yahvé, tu Dios, y él bendecirá tu pan y tu agua, y quitaré la enfermedad de en medio de ti.
Ku bauta wa Ubangiji Allahnku, albarkansa kuwa za tă kasance a kan abincinku da ruwan shanku. Zan ɗauke cuta daga cikinku.
26 Nadie abortará ni será estéril en tu tierra. Cumpliré el número de tus días.
A ƙasarku, mace ba za tă yi ɓari ba, ba kuma za a sami marar haihuwa ba. Zan ba ku tsawon rai.
27 Enviaré mi terror delante de ti y confundiré a todos los pueblos a los que vayas, y haré que todos tus enemigos te den la espalda.
“Zan aiki razanata a gabanku, in kuma sa ruɗami a cikin kowace al’ummar da za ku sadu da ita. Zan sa duk abokan gābanku su juye da baya, su gudu.
28 Enviaré el avispón delante de ti, que expulsará al heveo, al cananeo y al hitita de tu presencia.
Zan aiki rina a gabanku, su kori Hiwiyawa, Kan’aniyawa da kuma Hittiyawa.
29 No los expulsaré de delante de ti en un año, no sea que la tierra quede desolada y los animales del campo se multipliquen contra ti.
Amma ba a shekara guda zan kore muku su ba, don kada ƙasar tă zama kufai har namun jeji su fi ƙarfinku.
30 Poco a poco los expulsaré de delante de ti, hasta que te hayas multiplicado y hayas heredado la tierra.
Da kaɗan da kaɗan zan kore muku su, har yawanku yă kai yadda za ku mallaki ƙasar.
31 Fijaré tu frontera desde el Mar Rojo hasta el mar de los filisteos, y desde el desierto hasta el río; porque entregaré en tu mano a los habitantes de la tierra, y los expulsarás delante de ti.
“Zan kafa iyakokinku daga Jan Teku zuwa Bahar Rum, daga hamada kuma zuwa Kogi. Zan ba da mazaunan ƙasar a hannunku, za ku kuwa kore su daga gabanku.
32 No harás ningún pacto con ellos, ni con sus dioses.
Kada ku ƙulla yarjejjeniya da su, ko da allolinsu.
33 No habrán de habitar en tu tierra, para que no te hagan pecar contra mí, pues si sirves a sus dioses, ciertamente será una trampa para ti.”
Kada ku bari su zauna a cikin ƙasarku, in har kuka bar su, za su ɓata ku da zunubinsu na bautar allolinsu, har zai yă zama muku tarko.”