< Éxodo 2 >
1 Un hombre de la casa de Leví fue y tomó como esposa a una hija de Leví.
Ana nan, sai wani Balawe ya auri wata Balawiya,
2 La mujer concibió y dio a luz un hijo. Al ver que era un buen niño, lo escondió durante tres meses.
ta kuwa yi ciki, ta haifi ɗa. Sa’ad da ta ga jaririn kyakkyawa ne, sai ta ɓoye shi har watanni uku.
3 Cuando ya no pudo esconderlo, tomó un cesto de papiro para él, y lo cubrió con brea y alquitrán. Puso al niño en ella y lo depositó en los juncos de la orilla del río.
Amma da ba tă iya ɓoye shi kuma ba, sai ta yi kwandon kyauro ta shafa masa kwalta. Bayan haka sai ta sa jaririn a cikin kwandon, ta je ta ajiye kwandon tare da jaririn a cikin kyauro, a bakin kogin.
4 Su hermana se quedó lejos, para ver qué se hacía con él.
’Yar’uwarsa ta tsaya da ɗan rata tana lura da abin da zai faru da shi.
5 La hija del faraón bajó a bañarse en el río. Sus doncellas se paseaban por la orilla del río. Vio el cesto entre los juncos y envió a su criado a buscarlo.
Sai’yar Fir’auna ta gangara zuwa kogi domin tă yi wanka, bayinta kuwa suna tafiya a bakin kogi. Sai ta ga kwandon a ciyawa, ta aiki ɗaya daga cikin masu hidimarta tă ɗauko mata.
6 La abrió y vio al niño, y he aquí que el niño lloraba. Se compadeció de él y dijo: “Este es uno de los hijos de los hebreos”.
Da ta buɗe kwandon, sai ta ga yaro yana kuka, ta kuwa ji tausayinsa. Ta ce, “Wannan ɗaya daga cikin jariran Ibraniyawa ne.”
7 Entonces su hermana dijo a la hija del faraón: “¿Debo ir a llamar a una nodriza de las mujeres hebreas para que te amamante al niño?”
Sai’yar’uwarsa ta tambayi’yar Fir’auna, ta ce, “In tafi in samo ɗaya daga cikin matan Ibraniyawa tă yi miki renon yaron?”
8 La hija del faraón le dijo: “Ve”. La joven fue y llamó a la madre del niño.
Sai ta amsa ta ce, “I, tafi.” Sai yarinyar ta tafi ta kawo mahaifiyar yaron.
9 La hija del faraón le dijo: “Llévate a este niño y cuídalo por mí, y te daré tu salario”. La mujer tomó al niño y lo amamantó.
Diyar Fir’auna ta ce mata, “Ɗauki jaririn, ki yi mini renonsa, zan kuwa biya ki.” Saboda haka ta ɗauki yaron, ta yi renonsa.
10 El niño creció, lo llevó a la hija del faraón y se convirtió en su hijo. Ella le puso el nombre de Moisés, y dijo: “Porque lo saqué del agua”.
Sa’ad da ya yi girma, sai ta kawo shi wajen’yar Fir’auna, ya kuwa zama ɗanta, ta kuma ba shi suna Musa, tana cewa, “Na tsamo shi daga ruwa.”
11 En aquellos días, cuando Moisés había crecido, salió a ver a sus hermanos y vio sus cargas. Vio que un egipcio golpeaba a un hebreo, uno de sus hermanos.
Wata rana, bayan Musa ya yi girma, sai ya haura, ya tafi inda mutanensa suke, ya kuma ga yadda suke shan wahala da aiki. Ya ga wani mutumin Masar yana dūkan mutumin Ibraniyawa, ɗaya daga cikin mutanensa.
12 Miró a un lado y a otro, y al ver que no había nadie, mató al egipcio y lo escondió en la arena.
Da ya leƙa nan da can bai kuwa ga kowa ba, sai ya kashe mutumin Masar, ya ɓoye shi a yashi.
13 Salió el segundo día, y he aquí que dos hombres de los hebreos estaban peleando entre sí. Le dijo al que había hecho el mal: “¿Por qué golpeas a tu compañero?”.
Kashegari ya fita, sai ya ga Ibraniyawa biyu suna faɗa. Ya tambayi mai laifin ya ce, “Don me kake bugun ɗan’uwanka, mutumin Ibraniyawa?”
14 Él dijo: “¿Quién te ha hecho príncipe y juez sobre nosotros? ¿Piensas matarme, como mataste al egipcio?” Moisés tuvo miedo y dijo: “Ciertamente esto se sabe”.
Mutumin ya ce masa, “Wa ya mai da kai mai mulki da mai hukunci a kanmu? Kana so ne ka kashe ni kamar yadda ka kashe mutumin Masar nan?” Sai Musa ya tsorata, ya yi tunani ya ce, “To, fa, abin nan da na yi, ya zama sananne.”
15 Cuando el Faraón se enteró de esto, trató de matar a Moisés. Pero Moisés huyó de la presencia del Faraón, y vivió en la tierra de Madián, y se sentó junto a un pozo.
Da Fir’auna ya ji wannan, sai ya yi ƙoƙari yă kashe Musa, amma Musa ya gudu daga wajen Fir’auna, ya tafi ƙasar Midiyan inda ya zauna kusa da wata rijiya.
16 El sacerdote de Madián tenía siete hijas. Ellas vinieron y sacaron agua, y llenaron los abrevaderos para abrevar el rebaño de su padre.
To, fa, akwai wani firist na Midiyan, yana da’ya’ya mata bakwai, suka zo su shayar da dabbobin mahaifinsu.
17 Los pastores vinieron y las ahuyentaron; pero Moisés se levantó y las ayudó, y abrevó su rebaño.
Sai waɗansu makiyaya suka zo suka kore su, amma Musa ya tashi ya taimake su ya shayar da dabbobinsu.
18 Cuando llegaron a Reuel, su padre, éste les dijo: “¿Cómo es que habéis vuelto hoy tan temprano?”
Da’yan matan suka komo wurin Reyuwel mahaifinsu, sai ya tambaye su ya ce, “Yaya kuka dawo da wuri yau?”
19 Dijeron: “Un egipcio nos libró de la mano de los pastores, y además nos sacó agua y abrevó el rebaño.”
Suka amsa suka ce, “Wani mutumin Masar ne ya taimake mu daga hannun waɗansu makiyaya. Har ma ya ɗebo ruwa ya shayar da dabbobin.”
20 Dijo a sus hijas: “¿Dónde está? ¿Por qué habéis dejado al hombre? Llamadle, para que coma pan”.
Ya tambayi’yan matansa, “To ina yake? Don me kuka bar shi a can? A gayyace shi, yă zo, yă ci wani abu.”
21 Moisés se contentó con habitar con el hombre. Le dio a Moisés a Séfora, su hija.
Musa ya yarda yă zauna da mutumin wanda ya ba da’yarsa Ziffora aure da Musa.
22 Ella dio a luz un hijo, y él le puso el nombre de Gershom, porque dijo: “He vivido como extranjero en tierra extranjera”.
Ziffora ta haifi wa Musa ɗa, ya kuma raɗa masa suna Gershom cewa, “Na zama baƙo a baƙuwar ƙasa.”
23 En el transcurso de esos muchos días, el rey de Egipto murió, y los hijos de Israel suspiraron a causa de la esclavitud, y lloraron, y su clamor subió a Dios a causa de la esclavitud.
Ana nan dai, a kwana a tashi, sai sarkin Masar ya mutu. Isra’ilawa suka yi kuka mai zafi saboda bautarsu mai wuya, sai kukar neman taimakonsu saboda bauta, ya kai wurin Allah.
24 Dios oyó su gemido, y se acordó de su pacto con Abraham, con Isaac y con Jacob.
Allah kuwa ya ji kukansu sai ya tuna da alkawarinsa da Ibrahim da Ishaku da Yaƙub.
25 Dios vio a los hijos de Israel, y Dios comprendió.
Sai Allah ya dubi Isra’ilawa, ya kuma damu da su.