< Hechos 28 >
1 Cuando hubimos escapado, se enteraron de que la isla se llamaba Malta.
Bayan da muka kai bakin tekun lafiya, sai muka tarar cewa sunan tsibirin Malta ne.
2 Los nativos nos mostraron una amabilidad poco común, pues encendieron un fuego y nos recibieron a todos, a causa de la lluvia presente y del frío.
Mutanen tsibirin kuwa suka nuna mana babban alheri. Suka hura wuta suka marabce mu duka saboda ana ruwan sama da kuma sanyi.
3 Pero cuando Pablo reunió un manojo de palos y los puso sobre el fuego, una víbora salió a causa del calor y se le prendió en la mano.
Bulus ya tattara tarin itace, yayinda kuma yake sa itacen a wuta, sai maciji ya ɓullo saboda zafi, ya dāfe a hannunsa.
4 Cuando los nativos vieron la criatura colgando de su mano, se dijeron unos a otros: “Sin duda este hombre es un asesino, al que, aunque ha escapado del mar, la Justicia no ha dejado vivir.”
Da mutanen tsibirin suka ga macijin yana lilo a hannunsa, sai suka ce wa juna “Lalle, wannan mutum mai kisankai ne; gama ko da yake ya tsira daga teku, Adalci bai bar shi ya rayu ba.”
5 Sin embargo, él se sacudió la criatura en el fuego, y no sufrió ningún daño.
Amma Bulus ya karkaɗe macijin a cikin wuta, bai kuwa ji wani ciwo ba.
6 Pero ellos esperaban que se hubiera hinchado o que hubiera caído muerto de repente, pero cuando observaron durante mucho tiempo y vieron que no le ocurría nada malo, cambiaron de opinión y dijeron que era un dios.
Mutanen kuma suka yi zato zai kumbura ko kuma nan da nan zai fāɗi matacce, amma da aka daɗe ba su ga wani abu ya faru da shi ba, sai suka sāke ra’ayi suka ce shi wani allah ne.
7 En la vecindad de aquel lugar había tierras que pertenecían al jefe de la isla, llamado Publio, quien nos recibió y nos agasajó cortésmente durante tres días.
Akwai wani filin nan kusa wanda yake na Fubiliyus, babban shugaban tsibirin. Shi ne ya karɓe mu a gidansa da alheri ya kuma ciyar da mu har kwana uku.
8 El padre de Publio estaba enfermo de fiebre y disentería. Pablo entró en él, oró y, imponiéndole las manos, le sanó.
Mahaifinsa kuwa yana kwanciya a gado yana fama da zazzaɓi da atuni. Bulus ya shiga ciki don yă gan shi, bayan ya yi masa addu’a, sai ya ɗibiya masa hannuwa ya warkar da shi.
9 Hecho esto, vinieron también los demás enfermos de la isla y se curaron.
Sa’ad da wannan ya faru, sauran marasa lafiya a tsibirin suka zo aka kuma warkar da su.
10 También nos honraron con muchos honores; y cuando zarpamos, pusieron a bordo las cosas que necesitábamos.
Suka girmama mu ta kowane hali da muka shirya za mu tashi, sai suka ba mu abubuwan da muke bukata.
11 Al cabo de tres meses, zarpamos en una nave de Alejandría que había invernado en la isla, cuyo mascarón de proa era “Los hermanos gemelos”.
Bayan wata uku sai muka tashi a wani jirgin ruwan da ya ci damina a tsibirin. Jirgin ruwa kuwa na Alekzandariya ne yana da siffar tagwayen allolin Kasto da Follus.
12 Al llegar a Siracusa, permanecimos allí tres días.
Muka isa Sirakus a can muka yi kwana uku.
13 Desde allí dimos la vuelta y llegamos a Rhegium. Al cabo de un día, se levantó un viento del sur, y al segundo día llegamos a Puteoli,
Daga can muka tashi muka isa Regiyum. Kashegari iskar kudu ta taso, kashegari kuma muka kai Futeyoli.
14 donde encontramos hermanos, y nos rogaron que nos quedáramos con ellos siete días. Así llegamos a Roma.
A can muka tarar da waɗansu’yan’uwa waɗanda suka gayyaci mu mu yi mako ɗaya da su. Da haka dai muka kai Roma.
15 Desde allí, los hermanos, al saber de nosotros, salieron a nuestro encuentro hasta el Mercado de Apio y las Tres Tabernas. Al verlos, Pablo dio gracias a Dios y se animó.
’Yan’uwan da suke can sun sami labari cewa muna zuwa, sai suka tashi tun daga Kasuwar Affiyus da Masauƙi Uku don su tarye mu. Da ganin mutanen nan sai Bulus ya gode wa Allah ya kuma sami ƙarfafawa.
16 Cuando entramos en Roma, el centurión entregó los prisioneros al capitán de la guardia, pero a Pablo se le permitió quedarse solo con el soldado que lo custodiaba.
Da muka isa Roma, sai aka yarda wa Bulus yă zauna shi kaɗai, tare da sojan da zai yi gadinsa.
17 Al cabo de tres días, Pablo convocó a los jefes de los judíos. Cuando se reunieron, les dijo: “Yo, hermanos, aunque no había hecho nada contra el pueblo ni contra las costumbres de nuestros padres, fui entregado prisionero desde Jerusalén en manos de los romanos,
Bayan kwana uku sai ya kira taron shugabannin Yahudawa. Da suka taru, Bulus ya ce musu, “’Yan’uwana, ko da yake ban yi wa mutanenmu wani laifi ba ko kuma wani abu game da al’adun kakanninmu, aka kama ni a Urushalima aka kuma ba da ni ga Romawa.
18 los cuales, después de examinarme, quisieron ponerme en libertad, porque no había en mí ninguna causa de muerte.
Suka tuhume ni suka kuma so su sake ni, domin ba a same ni da wani laifin da ya cancanci kisa ba.
19 Pero cuando los judíos se pronunciaron en contra, me vi obligado a apelar al César, sin tener nada por lo que acusar a mi nación.
Amma da Yahudawa suka ƙi, sai ya zama mini dole in ɗaukaka ƙara zuwa gaban Kaisar ba don ina da wani zargin da zan kawo game da mutanena ba.
20 Por eso pedí verte y hablar contigo. Porque a causa de la esperanza de Israel estoy atado con esta cadena”.
Saboda wannan ne na nemi in gan ku in kuma yi magana da ku. Saboda begen Isra’ila ne, nake a daure da wannan sarƙa.”
21 Le dijeron: “No hemos recibido cartas de Judea acerca de ti, ni ninguno de los hermanos ha venido a informar o a hablar mal de ti.
Suka amsa cewa, “Ba mu sami wani wasiƙa daga Yahudiya game da kai ba, kuma ba kowa daga cikin’yan’uwan da suka zo daga can ya kawo wani labari ko ya faɗi wani mummuna abu game da kai.
22 Pero deseamos oír de ti lo que piensas. Porque, en cuanto a esta secta, nos consta que en todas partes se habla mal de ella.”
Amma muna so mu ji ra’ayinka, gama mun san cewa mutane ko’ina suna muguwar magana a kan wannan ɗarikar.”
23 Cuando le señalaron un día, acudió mucha gente a su alojamiento. Él les explicaba, testificando acerca del Reino de Dios, y persuadiéndolos acerca de Jesús, tanto de la ley de Moisés como de los profetas, desde la mañana hasta la noche.
Suka shirya su sadu da Bulus wata rana, suka ma zo da yawa fiye da dā a wurin da Bulus yake zama. Daga safe har zuwa yamma ya yi ta yin musu bayani, ya kuma shaida musu mulkin Allah yana ƙoƙarin rinjayarsu game da Yesu daga Dokar Musa da kuma daga Annabawa.
24 Algunos creyeron lo que se decía, y otros no creyeron.
Waɗansu suka rinjayu da abin da ya faɗa, amma waɗansu suka ba su gaskata ba.
25 Como no se ponían de acuerdo entre sí, se marchaban después de que Pablo había pronunciado un solo mensaje: “El Espíritu Santo habló correctamente por medio del profeta Isaías a nuestros padres,
Suka kāsa yarda da juna suka fara watsewa bayan Bulus ya yi wannan magana guda cewa, “Ruhu Mai Tsarki ya faɗa wa kakannin-kakanninku gaskiya sa’ad da ya ce ta bakin annabi Ishaya cewa,
26 diciendo, ‘Ve a este pueblo y dile, en la audición, oirás, pero no lo entenderá de ninguna manera. Al ver, verás, pero no percibirá de ninguna manera.
“‘Je ka wurin mutanen nan ka ce, “Za ku yi ta ji amma ba za ku fahimta ba; za ku yi ta dubawa, amma ba za ku gani ba.”
27 Porque el corazón de este pueblo se ha vuelto insensible. Sus oídos oyen con dificultad. Sus ojos se han cerrado. No sea que vean con sus ojos, oigan con sus oídos, entiendan con el corazón, y volvería a girar, entonces yo los sanaría’.
Gama zuciyar mutanen nan ta yi tauri; da ƙyar suke ji da kunnuwansu, sun kuma rufe idanunsu. In ba haka ba za su iya gani da idanunsu, su ji da kunnuwansu, su fahimta a zukatansu, su kuma juyo, in kuwa warkar da su.’
28 “Sabed, pues, que la salvación de Dios es enviada a las naciones, y ellas escucharán”.
“Saboda haka na so ku san cewa an aika da ceton Allah ga Al’ummai, za su kuwa saurara!”
29 Cuando dijo estas palabras, los judíos se marcharon, teniendo una gran disputa entre ellos.
30 Pablo permaneció dos años enteros en su propia casa alquilada y recibía a todos los que venían a él,
Shekaru biyu cif Bulus ya zauna a can a gidansa na haya yana marabtar duk wanda ya je wurinsa.
31 predicando el Reino de Dios y enseñando las cosas relativas al Señor Jesucristo con toda valentía, sin obstáculos.
Ya yi wa’azin mulkin Allah yana kuma koyarwa game da Ubangiji Yesu Kiristi, gabagadi ba tare da wani abu ya hana shi ba.