< Hechos 23 >

1 Pablo, mirando fijamente al consejo, dijo: “Hermanos, hasta hoy he vivido ante Dios con toda la buena conciencia.”
Bulus ya zuba wa Majalisar ido ya ce, “’Yan’uwana, na cika aikina ga Allah cikin lamiri mai kyau har yă zuwa yau.”
2 El sumo sacerdote, Ananías, ordenó a los que estaban junto a él que le golpearan en la boca.
Da jin wannan Ananiyas babban firist ya umarci waɗanda suke tsaye kusa da Bulus su buge bakinsa.
3 Entonces Pablo le dijo: “¡Dios te va a golpear a ti, muro blanqueado! ¿Te sientas a juzgarme según la ley, y mandas que me golpeen en contra de la ley?”
Sai Bulus ya ce masa, “Allah zai buge ka, kai farin bango! Ka zauna a can kana hukunta ni bisa ga doka, ga shi kai kanka kana ƙetare dokar ta wurin ba da umarni a buge ni!”
4 Los que estaban de pie dijeron: “¿Maltratas al sumo sacerdote de Dios?”
Waɗanda suke tsaye kusa da Bulus kuwa suka ce masa, “Babban firist na Allah za ka zaga?”
5 Pablo dijo: “No sabía, hermanos, que era sumo sacerdote. Porque está escrito: ‘No hablarás mal de un gobernante de tu pueblo’”.
Bulus ya amsa ya ce, “’Yan’uwa, ai, ban san cewa shi ne babban firist ba; gama yana a rubuce cewa, ‘Kada ka yi mugun magana game da mai mulkin mutanenka.’”
6 Pero cuando Pablo se dio cuenta de que una parte eran saduceos y la otra fariseos, gritó en el concilio: “Hombres y hermanos, yo soy fariseo, hijo de fariseos. En cuanto a la esperanza y la resurrección de los muertos estoy siendo juzgado”.
Bulus, da ya gane cewa waɗansu daga cikinsu Sadukiyawa ne sauran kuma Farisiyawa ne, sai ya ɗaga murya a Majalisar ya ce, “’Yan’uwana, ni Bafarisiye ne, ɗan Farisiyawa. Ana mini shari’a saboda begen da nake da shi a kan tashin matattu.”
7 Al decir esto, surgió una discusión entre fariseos y saduceos, y la multitud se dividió.
Da ya faɗi haka, sai gardama ta tashi tsakanin Farisiyawa da Sadukiyawa, taron kuwa ya rabu biyu.
8 Porque los saduceos dicen que no hay resurrección, ni ángel, ni espíritu; pero los fariseos confiesan todo esto.
(Sadukiyawa suna cewa babu tashin matattu, babu mala’iku ko ruhohi. Amma Farisiyawa kuwa sun tsaya a kan cewa duk akwai.)
9 Se armó un gran alboroto, y algunos de los escribas de la parte de los fariseos se levantaron y discutieron diciendo: “No encontramos ningún mal en este hombre. Pero si un espíritu o un ángel le ha hablado, ¡no luchemos contra Dios!”
Aka yi babbar hayaniya. Waɗansu daga cikin malaman dokokin da suke Farisiyawa suka miƙe tsaye suka yi gardama mai ƙarfi suna cewa, “Ba mu sami wani laifi a wurin mutumin nan ba. A ce wani ruhu ko mala’ika ne ya yi masa magana fa?”
10 Cuando se produjo una gran discusión, el oficial al mando, temiendo que Pablo fuera despedazado por ellos, ordenó a los soldados que bajaran y lo sacaran por la fuerza de entre ellos y lo llevaran al cuartel.
Gardamar kuwa ta yi tsanani har shugaban ƙungiyar sojan ya ji tsoro za su yayyage Bulus. Ya umarci sojoji su tafi su ƙwace shi ƙarfi da yaji daga wurinsu su kawo shi cikin barikin soja.
11 La noche siguiente, el Señor se puso a su lado y le dijo: “Anímate, Pablo, porque así como has dado testimonio de mí en Jerusalén, también debes darlo en Roma.”
Kashegari da dare Ubangiji ya tsaya kusa da Bulus ya ce, “Ka yi ƙarfin hali! Don kamar yadda ka yi shaida game da ni a Urushalima, haka kuma lalle, za ka yi shaidata a Roma.”
12 Cuando se hizo de día, algunos de los judíos se agruparon y se obligaron bajo una maldición, diciendo que no comerían ni beberían hasta que hubieran matado a Pablo.
Kashegari, Yahudawa suka ƙulla makirci suka kuma yi rantsuwa cewa ba za su ci ko sha ba sai sun kashe Bulus.
13 Eran más de cuarenta los que habían hecho esta conspiración.
Fiye da mutane arba’in ne suka ƙulla wannan makirci.
14 Se presentaron ante los jefes de los sacerdotes y los ancianos y dijeron: “Nos hemos obligado bajo una gran maldición a no probar nada hasta que hayamos matado a Pablo.
Suka je wajen manyan firistoci da dattawa suka ce, “Mun yi babbar rantsuwa cewa ba za mu ci kome ba sai mun kashe Bulus.
15 Ahora, pues, vosotros, con el consejo, informad al comandante para que lo haga bajar a vosotros mañana, como si fuerais a juzgar su caso con más exactitud. Estamos dispuestos a matarlo antes de que se acerque”.
Saboda haka, sai ku da Majalisa sai ku roƙi shugaban ƙungiyar sojan yă kawo shi a gabanku kamar kuna so ku ƙara samun cikakken bayani game da zancensa. Mu kuwa muna a shirye mu kashe shi kafin yă iso nan.”
16 Pero el hijo de la hermana de Pablo se enteró de que estaban al acecho y, entrando en el cuartel, se lo comunicó a Pablo.
Amma da ɗan’yar’uwar Bulus ya ji wannan makirci, sai ya tafi cikin barikin soja ya gaya wa Bulus.
17 Pablo llamó a uno de los centuriones y le dijo: “Lleva a este joven ante el oficial al mando, porque tiene algo que decirle.”
Sai Bulus ya kira ɗaya daga cikin jarumawan ya ce, “Ka kai wannan saurayi wurin shugaban ƙungiyar soja; yana da wani abin da zai faɗa masa.”
18 Así que lo tomó y lo llevó al oficial al mando y le dijo: “Pablo, el prisionero, me convocó y me pidió que le trajera a este joven. Tiene algo que decirle”.
Saboda haka ya ɗauke shi ya kai wajen shugaban ƙungiyar sojan. Jarumin ya ce, “Bulus, ɗan kurkukun nan ya kira ni, ya roƙe ni in kawo wannan saurayi a wurinka domin yana da wani abin da zai faɗa maka.”
19 El comandante le tomó de la mano y, apartándose, le preguntó en privado: “¿Qué es lo que tienes que decirme?”.
Sai shugaban ƙungiyar sojan ya kama hannun saurayin ya ja shi gefe, ya tambaye shi cewa, “Mene ne kake so ka gaya mini?”
20 Dijo: “Los judíos han acordado pedirte que mañana lleves a Pablo al consejo, como si tuvieran la intención de indagar algo más sobre él.
Saurayin ya ce, “Yahudawa sun ƙulla za su roƙe ka ka kawo Bulus a gaban Majalisa gobe kamar suna neman ƙarin cikakken bayani game da Bulus.
21 Por tanto, no cedas ante ellos, pues le acechan más de cuarenta hombres que se han obligado bajo maldición a no comer ni beber hasta que le hayan matado. Ahora están preparados, esperando la promesa de tu parte”.
Kada ka yarda da su, domin fiye da mutum arba’in daga cikinsu suna fakonsa. Sun yi rantsuwa ba za su ci ko sha ba sai sun kashe shi. Suna nan a shirye yanzu, suna jira ka amince da roƙonsu.”
22 Entonces el comandante dejó ir al joven, encargándole: “No digas a nadie que me has revelado estas cosas”.
Sai shugaban ƙungiyar sojan ya sallami saurayin ya kwaɓe shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa cewa ka faɗa mini wannan.”
23 Llamó a dos de los centuriones y les dijo: “Preparad doscientos soldados para ir hasta Cesarea, con setenta jinetes y doscientos hombres armados con lanzas, a la tercera hora de la noche.”
Sai ya kira biyu daga cikin jarumawansa, ya umarce su cewa, “Ku shirya sojoji ɗari biyu, da masu hawan dawakai saba’in da kuma masu māsu ɗari biyu su tafi Kaisariya da ƙarfe tara na daren nan.
24 Les pidió que le proporcionaran monturas, para que montaran a Pablo en una de ellas y lo llevaran sano y salvo a Félix, el gobernador.
Ku shirya wa Bulus dawakai da zai hau don a kai shi wurin Gwamna Felis lafiya.”
25 Escribió una carta como ésta:
Ya kuma rubuta wasiƙa kamar haka,
26 “Claudio Lisias al excelentísimo gobernador Félix: Saludos.
Kalaudiyus Lisiyas. Zuwa ga Mai Girma, Gwamna Felis. Gaisuwa.
27 “Este hombre fue apresado por los judíos y estaba a punto de ser asesinado por ellos, cuando llegué con los soldados y lo rescaté, tras saber que era romano.
Yahudawa sun kama wannan mutum suna kuma dab da kashe shi, amma na zo da sojojina na ƙwato shi, saboda na ji shi ɗan ƙasar Roma ne.
28 Deseando saber la causa por la que lo acusaban, lo llevé a su consejo.
Na so in san abin da ya sa suke zarginsa, saboda haka na kawo shi a gaban Majalisarsu.
29 Encontré que lo acusaban de cuestiones de su ley, pero no de nada digno de muerte o de prisión.
Na tarar cewa zargin da ake masa ya shafi waɗansu abubuwan da suka shafi dokarsu ne, amma ba wani zargi a kansa da ya isa kisa ko a daure shi.
30 Cuando me dijeron que los judíos estaban al acecho del hombre, lo envié inmediatamente a ti, encargando también a sus acusadores que presentaran sus acusaciones contra él ante ti. Adiós”.
Sa’ad da na sami labari cewa akwai wani makircin da aka ƙulla masa, sai na aika shi wurinka nan da nan. Na kuma umarci masu zarginsa su kai ƙararsu gare ka.
31 Así que los soldados, cumpliendo sus órdenes, tomaron a Pablo y lo llevaron de noche a Antipatris.
Saboda haka sojojin, don cika umarni, suka ɗauki Bulus da dad dare suka kawo shi har Antifatiris.
32 Pero al día siguiente dejaron a los jinetes que lo acompañaban y volvieron al cuartel.
Kashegari suka bar masu hawan dawakai suka ci gaba da shi, yayinda sojojin suka koma barikin soja.
33 Cuando llegaron a Cesarea y entregaron la carta al gobernador, también le presentaron a Pablo.
Sa’ad da masu hawan dawakai suka isa Kaisariya, sai suka ba wa gwamna wasiƙar suka kuma miƙa masa Bulus.
34 Cuando el gobernador la leyó, le preguntó de qué provincia era. Al comprender que era de Cilicia, dijo:
Gwamna ya karanta wasiƙar ya kuma tambaya ko daga wanda lardi ne ya fito. Da ya ji cewa shi daga Silisiya ne,
35 “Te escucharé plenamente cuando lleguen también tus acusadores”. Y ordenó que lo recluyeran en el palacio de Herodes.
sai ya ce, “Zan ji batunka lokacin da masu zarginka suka iso.” Sa’an nan ya ba da umarni a kai Bulus a tsare shi a fadar Hiridus.

< Hechos 23 >