< Hechos 18 >
1 Después de estas cosas, Pablo partió de Atenas y llegó a Corinto.
Bayan haka, Bulus ya bar Atens ya tafi Korint.
2 Encontró a un judío llamado Aquila, de raza del Ponto, que había llegado recientemente de Italia con su mujer Priscila, porque Claudio había ordenado a todos los judíos que salieran de Roma. Llegó a ellos,
A can ya sadu da wani mutumin Yahuda mai suna Akwila, ɗan garin Fontus, wanda ya je can ba da daɗewa ba daga Italiya tare da matarsa Firiskila, gama Kalaudiyus ya umarci dukan Yahudawa su bar Roma. Sai Bulus ya tafi yă gan su,
3 y como ejercía el mismo oficio, vivió con ellos y trabajó, pues de oficio eran fabricantes de tiendas.
da yake shi ma mai ɗinkin tenti ne kamar su, sai ya zauna ya yi aiki tare da su.
4 Todos los sábados razonaba en la sinagoga y persuadía a judíos y griegos.
Kowace Asabbaci kuwa yakan yi muhawwara a majami’a, yana ƙoƙari yă rinjayi Yahudawa da Hellenawa.
5 Cuando Silas y Timoteo bajaron de Macedonia, Pablo fue impulsado por el Espíritu, testificando a los judíos que Jesús era el Cristo.
Sa’ad da Sila da Timoti suka iso daga Makidoniya, sai Bulus ya ba da kansa ga yin wa’azi kaɗai, yana tabbatar wa Yahudawa cewa Yesu shi ne Kiristi.
6 Cuando se opusieron a él y blasfemaron, sacudió su ropa y les dijo: “¡Su sangre caiga sobre sus propias cabezas! Yo estoy limpio. A partir de ahora, iré a los gentiles”.
Amma sa’ad da Yahudawa suka yi hamayya da Bulus suka kuma shiga zaginsa, sai ya karkaɗe tufafinsa a cikin rashin yarda, ya ce musu, “Alhakinku yana a kanku! Ba ni da wani laifi. Daga yanzu zan tafi wajen Al’ummai.”
7 Salió de allí y entró en casa de un hombre llamado Justo, que adoraba a Dios, cuya casa estaba al lado de la sinagoga.
Sai Bulus ya bar majami’ar ya kuma tafi ƙofar da take kusa da gidan Titus Yustus, mai yi wa Allah sujada.
8 Crispo, el jefe de la sinagoga, creyó en el Señor con toda su casa. Muchos de los corintios, al oírlo, creyeron y se bautizaron.
Kirisbus, shugaban majami’a, da dukan iyalinsa suka gaskata Ubangiji; Korintiyawa masu yawa kuwa da suka ji shi suka gaskata, aka kuwa yi musu baftisma.
9 El Señor le dijo a Pablo en una visión nocturna: “No tengas miedo, habla y no te calles;
Wata rana da dad dare, Ubangiji ya yi magana da Bulus a cikin wahayi ya ce, “Kada ka ji tsoro; ka ci gaba da yin magana, kada ka yi shiru.
10 porque yo estoy contigo y nadie te atacará para hacerte daño, pues tengo mucha gente en esta ciudad.”
Gama ina tare da kai, ba kuma wanda zai fāɗa maka ya cuce ka, domin ina da mutane da yawa a wannan birni.”
11 Vivió allí un año y seis meses, enseñando la palabra de Dios entre ellos.
Saboda haka Bulus ya zauna a nan har shekara ɗaya da rabi, yana koya musu maganar Allah.
12 Pero cuando Galión era procónsul de Acaya, los judíos, de común acuerdo, se levantaron contra Pablo y lo llevaron ante el tribunal,
Yayinda Galliyo yake muƙaddas Akayya, Yahudawa suka haɗa kai suka tasar wa Bulus, suka kuwa kawo shi cikin kotu.
13 diciendo: “Este hombre persuade a los hombres a adorar a Dios en contra de la ley.”
Suka yi zarge cewa, “Wannan mutum yana rarrashin mutane su yi wa Allah sujada a hanyoyin da suka saɓa wa doka.”
14 Pero cuando Pablo estaba a punto de abrir la boca, Galión dijo a los judíos: “Si en verdad se tratara de un asunto incorrecto o de un delito inicuo, vosotros los judíos, sería razonable que yo os soportara;
A daidai sa’ad da Bulus yana shirin yin magana, sai Galliyo ya ce wa Yahudawan, “Da a ce ku Yahudawa kuna gunaguni game da munafunci, ko kuma wani babban laifi, da sai in iya sauraronku.
15 pero si se trata de cuestiones de palabras y nombres y de vuestra propia ley, miradlo vosotros mismos. Porque no quiero ser juez de estos asuntos”.
Amma da yake ya shafi gardama ce game da kalmomi da sunaye da kuma dokarku, sai ku ji da ita da kanku. Ni ba zan zama mai shari’a kan irin waɗannan abubuwa ba.”
16 Así que los expulsó del tribunal.
Saboda haka ya kore su.
17 Entonces todos los griegos agarraron a Sóstenes, el jefe de la sinagoga, y lo golpearon ante el tribunal. A Galio no le importó nada de esto.
Sai duk suka juya kan Sostenes shugaban majami’a suka yi masa dūka a gaban kotun. Amma Galliyo ko yă kula.
18 Después de esto, Pablo se despidió de los hermanos y se embarcó de allí hacia Siria, junto con Priscila y Aquila. En Cencreas se afeitó la cabeza, pues tenía un voto.
Bulus kuwa ya ci gaba da zama a Korint na’yan kwanaki. Sa’an nan ya bar’yan’uwa ya shiga jirgin ruwa zuwa Suriya tare da Firiskila da Akwila. Kafin ya tashi, ya aske kansa a Kenkireya saboda alkawarin da ya yi.
19 Llegó a Éfeso y los dejó allí; pero él mismo entró en la sinagoga y discutió con los judíos.
Suka isa Afisa, inda Bulus ya bar Firiskila da Akwila. Shi kansa ya shiga majami’a ya kuma yi muhawwara da Yahudawa.
20 Cuando le pidieron que se quedara con ellos más tiempo, lo rechazó;
Sa’ad da suka roƙe shi ya ƙara’yan kwanaki da su, bai yarda ba.
21 pero despidiéndose de ellos, les dijo: “Tengo que celebrar esta próxima fiesta en Jerusalén, pero volveré de nuevo a vosotros si Dios quiere.” Entonces partió de Éfeso.
Amma da yake barin wurin, ya yi alkawari cewa, “Zan dawo in Allah ya yarda.” Sa’an nan ya tashi daga Afisa a jirgin ruwa.
22 Cuando desembarcó en Cesarea, subió a saludar a la asamblea y bajó a Antioquía.
Sa’ad da ya sauka a Kaisariya, sai ya haura ya gai da ikkilisiya sa’an nan ya gangara zuwa Antiyok.
23 Después de pasar algún tiempo allí, partió y recorrió por orden la región de Galacia y Frigia, estableciendo a todos los discípulos.
Bayan ya yi’yan kwanaki a Antiyok, Bulus ya tashi daga can ya zaga ko’ina a yankin Galatiya da Firjiya, yana ƙarfafa dukan almajirai.
24 Llegó a Éfeso un judío llamado Apolos, de raza alejandrina, hombre elocuente. Era poderoso en las Escrituras.
Ana cikin haka sai wani mutumin Yahuda mai suna Afollos, ɗan ƙasar Alekzandariya, ya zo Afisa. Shi masani ne, yana da cikakken sani na Nassosi.
25 Este hombre había sido instruido en el camino del Señor; y siendo ferviente de espíritu, hablaba y enseñaba con exactitud las cosas relativas a Jesús, aunque sólo conocía el bautismo de Juan.
An horar da shi a hanyar Ubangiji, ya kuma himma ƙwarai a magana, ya kuma yi koyarwa game da Yesu, daidai, ko da yake baftismar Yohanna ce kaɗai ya sani.
26 Comenzó a hablar con valentía en la sinagoga. Pero cuando Priscila y Aquila le oyeron, le llevaron aparte y le explicaron con más precisión el camino de Dios.
Sai ya fara magana gabagadi a majami’a. Sa’ad da Firiskila da Akwila suka ji shi, sai suka gayyace shi gidansu suka ƙara bayyana masa hanyar Allah sosai.
27 Cuando decidió pasar a Acaya, los hermanos le animaron y escribieron a los discípulos para que le recibieran. Cuando llegó, ayudó mucho a los que habían creído por medio de la gracia;
Sa’ad da Afollos ya so ya tafi Akayya, sai’yan’uwa suka ƙarfafa shi suka kuma rubuta wa almajiran da suke can da su marabce shi. Da isowarsa, ya zama da taimako ƙwarai ga waɗanda ta wurin alheri suka gaskata.
28 pues refutó poderosamente a los judíos, mostrando públicamente con las Escrituras que Jesús era el Cristo.
Gama da ƙwazo ya ƙaryata Yahudawa a muhawwara a fili, yana tabbatar daga Nassosi cewa Yesu shi ne Kiristi.