< 2 Crónicas 14 >
1 Así que Abías durmió con sus padres, y lo enterraron en la ciudad de David; y su hijo Asa reinó en su lugar. En sus días, la tierra estuvo tranquila diez años.
Abiya kuwa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Asa ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki, a zamaninsa kuma ƙasar ta zauna lafiya na shekara goma.
2 Asá hizo lo que era bueno y correcto a los ojos de Yahvé, su Dios,
Asa ya yi abin da yake da kyau da kuma daidai a gaban Ubangiji Allahnsa.
3 pues quitó los altares extranjeros y los lugares altos, derribó las columnas, cortó los postes de Asera,
Ya kawar da baƙin bagade da masujadai bisa tudu, ya farfashe keɓaɓɓun duwatsu, ya kuma sassare ginshiƙan Ashera.
4 y ordenó a Judá que buscara a Yahvé, el Dios de sus padres, y que obedeciera su ley y su mandato.
Ya umarci Yahuda su nemi Ubangiji Allah na kakanninsu, su kuma yi biyayya da dokoki da kuma umarnansa.
5 También quitó de todas las ciudades de Judá los lugares altos y las imágenes del sol, y el reino quedó tranquilo ante él.
Ya kawar da masujadan kan tudu da bagadan turare a kowane gari a Yahuda, masarautar kuwa ta zauna lafiya a ƙarƙashinsa.
6 Edificó ciudades fortificadas en Judá, pues la tierra estaba tranquila, y no tuvo guerras en esos años, porque el Señor le había dado descanso.
Ya gina biranen katanga na Yahuda, da yake ƙasar tana zaman lafiya. Babu wanda yake yaƙi da shi a waɗannan shekaru, gama Ubangiji ya ba shi hutu.
7 Pues dijo a Judá: “Construyamos estas ciudades y hagamos muros alrededor de ellas, con torres, puertas y rejas. La tierra está aún ante nosotros, porque hemos buscado a Yahvé, nuestro Dios. Lo hemos buscado, y él nos ha dado descanso por todos lados”. Así construyeron y prosperaron.
Ya ce wa Yahuda, “Bari mu gina waɗannan garuruwa mu sa katanga kewaye da su, da hasumiyoyi, ƙofofi da ƙyamare. Ƙasar har yanzu tamu ce domin mun nemi Ubangiji Allahnmu, mun neme shi ya kuwa ba mu hutu a kowane gefe.” Saboda haka suka gina suka kuma yi nasara.
8 Asá tenía un ejército de trescientos mil de Judá, que llevaban escudos y lanzas, y doscientos ochenta mil de Benjamín, que llevaban escudos y tensaban arcos. Todos ellos eran hombres de gran valor.
Asa ya kasance da mayaƙa dubu ɗari uku daga Yahuda, kintsatse da manyan garkuwoyi da māsu, da kuma mayaƙa dubu ɗari biyu da dubu tamanin daga Benyamin, riƙe da ƙananan garkuwoyi da kuma baka. Dukan waɗannan jarumawa ne ƙwarai.
9 Zéraj el etíope salió contra ellos con un ejército de un millón de soldados y trescientos carros, y llegó a Maresá.
Zera mutumin Kush ya taka ya fita don yă yaƙe su da babban runduna da kuma kekunan yaƙi ɗari uku, ya kuma zo har Maresha.
10 Asá salió a su encuentro, y prepararon la batalla en el valle de Cefatá, en Maresá.
Asa ya fita don yă ƙara da shi, suka ja dāgā yaƙi a Kwarin Zefata kusa da Maresha.
11 Asá clamó a su Dios, y dijo: “Señor, no hay nadie más que tú para ayudar, entre el poderoso y el que no tiene fuerza. Ayúdanos, Yahvé, nuestro Dios, porque en ti confiamos, y en tu nombre venimos contra esta multitud. Yahvé, tú eres nuestro Dios. No dejes que el hombre prevalezca contra ti”.
Sai Asa ya kira ga Ubangiji Allahnsa ya ce, “Ubangiji, babu wani kamar ka da zai taimaki marar ƙarfi a kan mai ƙarfi. Ka taimake mu, ya Ubangiji Allahnmu, gama mun dogara a gare ka, kuma a cikin sunanka muka fito don mu yaƙi wannan babbar runduna. Ya Ubangiji, kai ne Allahnmu; kada ka bar mutum yă yi nasara a kanka.”
12 El Señor hirió a los etíopes ante Asa y ante Judá, y los etíopes huyeron.
Ubangiji fa ya bugi mutanen Kush a gaban Asa da Yahuda. Mutanen Kush suka gudu,
13 Asá y el pueblo que estaba con él los persiguieron hasta Gerar. Fueron tantos los etíopes que cayeron que no pudieron recuperarse, pues fueron destruidos ante el Señor y ante su ejército. El ejército de Judá se llevó mucho botín.
Asa kuwa da mayaƙansa suka bi su har Gerar. Mutanen Kush suka mutu a ranan nan har ba a iya ƙidaya, aka buge su a gaban Ubangiji da rundunansa. Mutanen Yahuda suka kwashi ganima sosai.
14 Atacaron todas las ciudades alrededor de Gerar, porque el temor de Yahvé se apoderó de ellas. Saquearon todas las ciudades, pues había mucho botín en ellas.
Suka hallaka dukan ƙauyukan kewaye da Gerar, gama tsoron Ubangiji ya kama su. Suka kwashi ganima na dukan ƙauyukan nan, da yake akwai ganima sosai a can.
15 También atacaron las tiendas de los que tenían ganado, y se llevaron ovejas y camellos en abundancia, y luego regresaron a Jerusalén.
Suka kuma yaƙi sansanin makiyaya suka kwashe tumaki da awaki da raƙuma. Suka koma Urushalima.