< Salmos 78 >
1 Un salmo (masquil) de Asaf. Escucha, pueblo mío, lo que tengo para enseñarte. Escucha lo que vengo a decirte.
Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
2 Te enseñaré dichos sabios; y te explicaré misterios del pasado
Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
3 que he escuchado antes y sobre los cuales he reflexionado. Son historias de nuestros antepasados que han sido transmitidas por generaciones.
abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
4 No las ocultaremos de nuestros hijos. Le contaremos a la siguiente generación sobre las maravillas que Dios ha hecho; sobre su poder y grandes obras.
Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
5 Él entregó sus leyes a los descendientes de Jacob; dio sus instrucciones al pueblo de Israel. Él ordenó a nuestros padres para que las enseñaran a sus hijos,
Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
6 a fin de que la siguiente generación—los que aún no habían nacido—entendieran y crecieran para enseñar a sus hijos.
don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
7 De esta forma debían mantener su fe en Dios y no olvidar lo que Dios ha hecho, así como seguir sus mandamientos.
Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
8 Para que no fueran como sus antepasados, una generación terca y rebelde que carecía de fe y fidelidad.
Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
9 Los soldados de Efraín, aunque estaban armados con arcos, huyeron el día de la batalla.
Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
10 No cumplieron el pacto de Dios, y se negaron a seguir sus leyes.
ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
11 Ignoraronl lo que Dios había hecho, y las maravillas que les había mostrado antes:
Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
12 los milagros que había hecho por sus antepasados en Zoán, en Egipto.
Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
13 Él dividió el mar en dos y los condujo a través de él, manteniendo las aguas como muros a cada lado.
Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
14 Él los guiaba con una nube en el día, y de noche con una nube de fuego.
Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
15 Partió las rocas en el desierto para darle agua abundante a su pueblo. Aguas profundas como el océano.
Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
16 ¡Él hizo que de las piedras fluyera agua como un río!
ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
17 Pero ellos siguieron pecando contra él, rebelándose contra el Altísimo mientras andaban por el desierto.
Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
18 Deliberadamente provocaban a Dios, exigiendo las comidas que tanto anhelaban.
Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
19 Insultaron a Dios diciendo: “¿Puede Dios darnos comida aquí en el desierto?
Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
20 Si bien puede golpear una roca y hacer que de ellas fluya agua como corrientes de río, ¿puede acaso darnos pan? ¿Puede darnos carne?”
Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
21 Cuando el Señor oyó esto, se enojó mucho, y el fuego de su enojo se encendió contra los descendientes de Jacob, el pueblo de Israel,
Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
22 porque ellos no creyeron en Dios y no confiaron en que podía cuidar de ellos.
gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
23 Tanto fue su enojo que ordenó a los cielos se abrieran,
Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
24 e hizo llover maná del cielo, dándoles así pan celestial.
ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
25 Los seres humanos comieron del pan que comen los ángeles. Y les dio más que suficiente.
Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
26 Luego hizo soplar un viento desde el Este, y por su poder también hizo soplar el viento que viene del Sur.
Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
27 Hizo llover carne como tan abundante como el polvo. Las aves eran muchas, como la arena de la playa.
Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
28 E hizo caer las aves en medio del campamento, y alrededor de sus carpas.
Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
29 Y comieron hasta que se saciaron. Les dio la comida que tanto deseaban.
Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
30 Pero antes de saciar su apetito, mientras aún masticaban la carne,
Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
31 Dios se enojó con ellos e hizo morir a los hombres más fuertes, derribándolos en plena juventud.
fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
32 A pesar de esto, siguieron pecando. A pesar de los milagros, se negaban a creer en él.
Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
33 Así que apagó sus vidas vanas, e hizo que terminaran sus años con horror.
Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
34 Cuando Dios comenzó a matarlos, volvieron con oraciones a él, arrepentidos de su pecado.
A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
35 Se acordaron de que Dios era su roca, que el Dios Altísimo era su salvador.
Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
36 Entonces lo comenzaron adular de labios para afuera, pero solo mentían.
Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
37 En sus corazones no eran sinceros y no guardaron el pacto que tenían con él.
zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
38 Pero por su compasión él perdonó su pecado y no los destruyó. Muchas veces contuvo su enojo y no desató toda su furia.
Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
39 Dios recordó que eran simples mortales, y que eran como el viento que se va y no regresa.
Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
40 Cuántas veces se rebelaron contra él en el desierto, causándole tristeza.
Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
41 Una y otra vez provocaron a Dios, causando dolor al Santo de Israel.
Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
42 Olvidaron la fuerza con la que él los rescató de sus opresores,
Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
43 haciendo milagros en Egipto, y maravillas en la llanura de Zoán.
ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
44 Allí convirtió sus ríos y fuentes de agua en sangre, de modo que nadie podía beber de ellos.
Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
45 Envió moscas para destruirlos, y ranas para que los arruinaran.
Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
46 Dio sus cultivos a las langostas, y todo el fruto de su trabajo fue devorado por ellas.
Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
47 Destruyó sus viñedos con granizo, y sus higueras con aguanieve.
Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
48 Dejó su ganado a merced del granizo y sus animales fueron destruidos por relámpagos.
Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
49 Envió sobre ellos su ira feroz: Rabia, hostilidad y agonía. Por ello envió un grupo de ángeles destructores.
Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
50 Desató su ira sobre ellos y no los salvó de la muerte, sino que los dejó morir por causa de esta plaga.
Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
51 Entonces mató al hijo mayor de cada familia en Egipto, todos los que habían sido concebidos como primogénitos en las carpas de Ham.
Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
52 Pero a su pueblo guió como ovejas, y los condujo como un rebaño en el desierto.
Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
53 Los llevó a un lugar seguro, y no tuvieron nada que temer. Ahogó a sus enemigos en el mar.
Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
54 Los llevó hasta la frontera de su tierra santa, a esta tierra montañosa que había conquistado para ellos.
Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
55 A las naciones infieles las expulsaba a su paso. Dividió la tierra para que la hicieran suya. Estableció las tribus de Israel en sus carpas.
Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
56 Pero ellos siguieron provocando al Altísimo, siendo rebeldes contra él. No siguieron sus enseñanzas.
Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
57 Así como sus antiguos padres se alejaron de Dios y fueron infieles a él, tan torcidos como un arco doblado que no sirve.
Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
58 Provocaron su ira con sus altares paganos y despertaron su celo con sus ídolos.
Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
59 Cuando Dios escuchó que adoraban a otros dioses se enfureció y rechazó por completo a Israel.
Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
60 Entonces abandonó su lugar en Siloé, el Tabernáculo en el que vivía en medio del pueblo.
Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
61 Además entregó el arca de su poder, dejando que manos enemigas la tomaran.
Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
62 Entregó a su pueblo y permitió que lo masacraran a espada, pues estaba furioso con su pueblo escogido.
Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
63 Sus hombres más jóvenes fueron quemados, y las mujeres jóvenes no lograron cantar sus cánticos de bodas.
Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
64 Sus sacerdotes fueron asesinados con espadas y sus viudas no pudieron hacer duelo por ellos.
aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
65 Entonces el Señor reaccionó como si hubiera despertado del sueño, como un guerrero que se despierta después de embriagarse con vino.
Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
66 Venció a sus enemigos, atacándolos por la espalda y exponiéndolos a vergüenza eterna.
Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
67 Rechazó a los descendientes de José y no elegió más a la tribu de Eraín.
Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
68 En su lugar eligió a la tribu de Judá y al Monte de Sión, al cual amaba.
amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
69 Allí construyó su santuario, tan alto como el cielo, y lo puso allí en esa tierra para que existiera eternamente.
Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
70 Eligió a su siervo David, tomándolo de entre los rediles de ovejas,
Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
71 y lo llevó de cuidar ovejas y corderos, a ser un pastor de los descendientes de Jacob, el pueblo especial de Dios: Israel.
daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
72 Como un pastor cuidó de ellos con sincera devoción, y los condujo con manos hábiles.
Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.