< Salmos 66 >
1 Para el director del coro. Una canción. Un salmo. ¡Toda la tierra eleve su voz con alegría a Dios!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
2 Canten sobre su maravilloso nombre. ¡Alábenle por su bondad!
Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
3 Digan a Dios: “¡Grandes son tus maravillas! ¡Tus enemigos se arrodillan ante ti por causa de tu poder!
Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
4 Todos en la tierra te adoran, y cantan alabanzas a ti. Te adoran por quien eres”. (Selah)
Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
5 ¡Vengan y vean lo que Dios ha hecho! ¡Lo que Dios hace por su pueblo es maravilloso!
Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
6 Él transformó el Mar Rojo en tierra seca, y su pueblo caminó entre las aguas. Celebramos por lo que hizo.
Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
7 Él gobierna para siempre con su poder. Él cuida de las naciones, y vigila que ningún rebelde se levante en oposición. (Selah)
Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
8 Que todos los pueblos de la tierra bendigan a nuestro Dios y canten a gritos alabanzas a él.
Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
9 Él nos ha mantenido con vida, y no nos ha dejado caer.
ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
10 Dios, tú nos has examinado, y nos has refinado como la plata.
Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
11 Tú nos has atrapado en tu red, y has puesto pesada carga sobre nosotros.
Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
12 Dejas que las personas nos pisoteen con rudeza; Hemos pasado por fuego e inundaciones, pero tú nos has traído a un lugar seguro.
Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
13 Me presentaré en tu Templo con sacrificios. Cumpliré mis promesas hacia ti,
Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
14 esas promesas que hice cuando estuve en momentos de dificultad.
alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
15 Haré sacrificios de becerros gordos, subirá el humo del sacrificio de carneros, ofrendas de toros y cabras. (Selah)
Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
16 Vengan y escuchen, todos los que honran a Dios, y yo les contaré todas las cosas que ha hecho por mi.
Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
17 Yo clamé a él y le alabé con mi voz.
Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
18 Si hubiera tenido pecado en mi pensamiento, el Señor no me habría escuchado.
Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
19 ¡Pero Dios me escuchó! ¡Escuchó mi oración!
amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
20 Alaben a Dios, quien no ignoró mi oración ni me retiró su amor.
Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!