< Salmos 50 >

1 Un Salmo de Asaf. ¡El Señor, el Dios todopoderoso, habla! Él convoca a todos en la tierra, desde el este hasta el oeste.
Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
2 Dios brilla desde el monte de Sión, perfecto en belleza.
Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
3 Nuestro Dios llegará, y no se quedará quieto. Llamas de fuego vienen detrás de él, quemando todo a su alrededor; una feroz tormenta se mueve alrededor de él.
Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
4 Invoca a los cielos sobre la tierra para que presencien el juicio de su pueblo.
Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
5 “Tráiganme a los que confían en mí, aquellos que cumplieron mi pacto conmigo como sacrificio”.
“Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
6 Los cielos declaran que sus decisiones están bien, porque Dios mismo es el juez. (Selah)
Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
7 “Mi pueblo, escuchen lo que tengo para decir. Traigo cargos en su contra, Israel. ¡Yo soy Dios, su Dios!
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
8 No estoy hablando de sacrificios ni de ofrendas quemadas que me ofrecen todo el tiempo.
Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
9 No necesito toros de sus graneros ni cabras de sus corrales,
Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
10 porque míos son todos los animales del bosque, y el ganado de miles de cerros me pertenece.
gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
11 Conozco a cada pájaro de la montaña; todas las cosas vivientes en los campos son mías.
Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
12 Si estuviera hambriento, no te lo diría, porque la tierra y todo lo que hay en ella es mío.
Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
13 ¿Me como yo la carne de los toros y bebo la sangre de las cabras?
Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
14 Den ofrendas de agradecimiento a Dios; mantengan las promesas que le hicieron al Altísimo,
“Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
15 y llámenme cuando estén en problemas. Los rescataré, y me agradecerán”.
ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
16 Pero a los malvados Dios les dice, “¿Cuál es el objetivo de repetir mi ley y hacer promesas vacías sobre obedecer mi pacto?
Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
17 Odias mi disciplina, y desechas mis palabras.
Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
18 Cuando ves a la gente robando los admiras y te asocias con adúlteros.
Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
19 Con tu boca dices cosas malas; usas tu lengua para esparcir mentiras.
Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
20 Te sientas y comienzas a hablar en contra de tu hermano, calumniando al hijo de tu propia madre.
Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
21 Yo me quedo callado cuando haces esas cosas. Tú pensaste que yo era alguien como tú. Pero ahora te confronto, y traigo mis cargos en contra tuya.
Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
22 Piensen otra vez, ustedes que menosprecian a Dios, o los haré trizas, y nadie podrá salvarlos.
“Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
23 Pero aquellos que dan ofrendas de agradecimiento me honran, y a aquellos que siguen el bien les mostraré mi salvación”.
Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”

< Salmos 50 >