< Salmos 47 >

1 Para el director del coro. Un Salmo de los hijos de Coré. ¡Aplauda todo el mundo! ¡Griten con alegría al Señor!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
2 Porque nuestro Señor Altísimo es imponente; él es el gran rey de toda la tierra.
Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
3 Él somete a los otros pueblos bajo nosotros; pone a las naciones bajo nuestros pies.
Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
4 Él escogió la tierra prometida para nosotros; la orgullosa posesión de los descendientes de Jacob a quienes ama. (Selah)
Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
5 Dios asciende a su trono con grandes gritos, el Señor es acompañado con el sonido de trompetas.
Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
6 ¡Canten alabanzas a Dios, canten, canten alabanzas a nuestro Rey, canten!
Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
7 ¡Porque el Señor es el Rey de toda la tierra; canten alabanzas con Salmos!
Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
8 Dios gobierna sobre las naciones; se sienta sobre su santo trono.
Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
9 Los gobernantes de las naciones se reúnen junto con la gente del Dios de Abraham, porque los defensores de la tierra le pertenecen a Dios. Él será honrado por toda la tierra.
Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.

< Salmos 47 >