< Salmos 44 >

1 Para el director del coro. Un salmo (masquil) de los hijos de Coré. Dios, hemos escuchado con nuestros propios oídos, nuestros antepasados nos han dicho todo lo que tú hiciste en sus épocas, mucho tiempo atrás.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
2 Con tu poder quitaste del camino a las otras naciones, estableciste a nuestros antepasados en el lugar que les pertenecía; derrotaste a las naciones y enviaste a nuestros ancestros a ocupar la tierra que les habías prometido.
Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
3 No conquistaron la tierra con sus espadas; no fue a través de su fuerza que ganaron la victoria, fue por tu fuerza, tu poder, y tu compañía, porque los amabas.
Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
4 Dios, tú eres mi rey. ¡Nos diste victorias en nombre de Jacob!
Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
5 Solo a través de ti podemos ahuyentar a nuestros enemigos. Solo en tu nombre podemos derrotar a nuestros oponentes.
Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
6 No confío en mi arco; no creo que mi espada vaya a salvarme.
Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
7 Tú eres el único que nos salva de nuestros enemigos; acabas con aquellos que nos odian.
amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
8 Dios, te alabamos gozosos todo el día y alabamos tu nombre. (Selah)
A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
9 Pero ahora nos has rechazado y has apartado tu gracia de nosotros; has abandonado a nuestros ejércitos.
Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
10 Nos has hecho correr huyendo de nuestros enemigos, y quienes nos odian se han llevado todo lo que han querido.
Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
11 Nos has entregado como una oveja que va al sacrificio; nos has escatimado en frente de las otras naciones.
Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
12 Has vendido a tu propio pueblo por el precio de nada, no haciendo ni una sola queja al momento de la venta.
Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
13 Te has burlado de nosotros en frente de nuestros prójimos, somos ridiculizados y burlados por todos los que están a nuestro alrededor.
Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
14 Nos has vuelto un chiste para las otras naciones; sacuden con fuerza sus manos ante nosotros.
Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
15 Somos humillados el día entero; escondemos nuestras cabezas por la vergüenza,
Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
16 por todos los insultos de las personas que se burlan de nosotros, porque nuestros enemigos vengativos están justo detrás de nosotros.
saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
17 Todo esto nos ha pasado incluso aunque nunca te olvidamos; no hemos sido infieles a las promesas que nos has hecho.
Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
18 No nos hemos alejado de ti, ni en pensamientos, ni en acciones.
Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
19 Pero tú nos aplastaste, y nos convertiste en guarida de chacales. Nos has cubierto con la oscuridad de la muerte.
Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
20 Si hemos olvidado el nombre de nuestro Dios, o hemos adorado a otros dioses,
Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
21 ¿No lo sabría Dios, siendo que él conoce los pensamientos de todos?
da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
22 Pero por tu culpa nos matan día y noche. Somos considerados solo como ovejas listas para el sacrificio.
Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
23 ¡Despiértate Señor! ¿Por qué estás durmiendo? ¡Levántate! ¡No nos des la espalda por siempre!
Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
24 ¿Por qué apartas tu vista de nosotros y no de tas cuenta de nuestra miseria y sufrimiento?
Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
25 Caemos arruinados al polvo, nuestros cuerpos caen de cara al mugre.
An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
26 ¡Levántate! ¡Ven y ayúdanos! ¡Sálvanos por la gracia de tu misericordioso amor!
Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.

< Salmos 44 >