< Salmos 38 >

1 Un Salmo de David, pidiendo a Dios que se acuerde de él. ¡Señor, por favor no me condenes, por causa de tu enojo conmigo! ¡No me castigues con tu furia!
Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
2 Tus flechas me han atravesado, tus manos han caído sobre mí.
Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
3 Por tu enojo hacia mí, ni una sola parte de mi cuerpo está sana. Estoy completamente enfermo por mis pecados.
Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
4 Me estoy ahogando en culpa. La carga es muy pesada de llevar.
Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
5 Mis heridas están infectadas, están comenzando a oler mal, y por culpa de mi terquedad.
Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
6 Estoy encorvado, retorcido por el dolor. Camino el día entero llorando y lamentándome.
An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
7 Estoy ardiendo por dentro de fiebre. Ninguna parte de mi cuerpo está sana.
Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
8 Estoy muy cansado, totalmente deshecho. Siento mi corazón como ruge de angustia.
Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
9 Señor, sabes lo que quiero desesperadamente, escuchas cada respiración que tomo.
Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
10 Mi corazón se está acelerando, dejándome sin fuerza. Mi vista está decayendo.
Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
11 Mis amados y amigos no se me acercan porque tienen miedo de contagiarse. Incluso mi familia se ha distanciado.
Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
12 Aquellos que intentan matarme me ponen trampas. Los que intentan herirme me amenazan, trabajando en sus planes engañosos todo el día.
Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
13 Yo actúo como si fuera sordo con sus palabras, e intento parecer tonto para no tener que hablar.
Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
14 Como un hombre que no puede oír, y que no responde, ¡Ese soy yo!
Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
15 ¡Porque espero en ti, Señor! Tú me responderás, Dios mío.
Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
16 Señor, te pido que por favor mis enemigos no se jacten en frente mí, no dejes que se alegren cuando yo tropiece.
Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
17 Porque estoy por colapsar, el dolor nunca se detiene.
Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
18 Confieso mis pecados. Lamento horriblemente todo lo que he hecho.
Na furta laifina; na damu da zunubina.
19 Tengo enemigos muy poderosos, son bastante activos, y me odian sin razón.
Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
20 Me pagan el bien con mal. Me acusan por el bien que he tratado de hacer.
Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
21 Señor, no me abandones, no te alejes de mí.
Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
22 Apresúrate, ven y ayúdame, ¡Oh, Señor, mi salvador!
Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.

< Salmos 38 >