< Salmos 130 >
1 Un cántico para los peregrinos que van a Jerusalén. Señor, clamo a ti desde lo más profundo de mi dolor.
Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
2 Por favor escucha mi llanto, presta atención a lo que pido.
Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
3 Señor, si guardaras una lista de nuestros pecados, ¿Quién podría escapar de ser condenado?
In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
4 Pero tú eres un Dios perdonador y por eso debes ser respetado.
Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
5 Yo espero en el Señor, espero ansiosamente, porque confío en su palabra.
Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
6 Anhelo que el Señor vuelva, más que los vigilantes añorando el amanecer.
Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
7 Israel, deposita tus esperanzas en el Señor, porque el Señor nos ama con su inmenso amor, y su salvación no conoce límites.
Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
8 Él redimirá a Israel de todos sus pecados.
Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.