< Salmos 120 >
1 Un cántico para los peregrinos que van a Jerusalén. Clamé al Señor en medio de todas mis tribulaciones, y Él me contestó.
Waƙar haurawa. Na yi kira ga Ubangiji cikin damuwata, ya kuwa amsa mini.
2 ¡Señor, por favor sálvame de los mentirosos y de los engañadores!
Ka cece ni, ya Ubangiji, daga leɓuna masu ƙarya da kuma daga harsuna masu yaudara.
3 ¿Qué hará el Señor con ustedes, mentirosos? ¿Cómo los castigará?
Me zai yi maka, me kuma ya fi, ya kai harshe mai yaudara?
4 Con la espada afilada de un guerrero y carbones encendidos de un enebro.
Zai hukunta ku da kibiyoyi masu tsini na jarumi, tare da garwashin wuta na itacen tsintsiya.
5 ¡Ay de mí! Que soy extranjero en Meséc, que he acampado entre las tiendas de Cedar.
Kaitona da nake zama a Meshek, da nake zama a ciki tentunan Kedar!
6 He vivido por mucho tiempo entre los pueblos que odian la paz.
Da daɗewa na zauna a cikin waɗanda suke ƙin salama.
7 Quiero paz, pero cuando hablo de paz, ellos quieren guerra.
Ni mutum ne mai salama; amma sa’ad da na yi magana, su sai su yi ta yaƙi.