< Salmos 119 >

1 Felices son los que hacen lo recto y siguen las enseñanzas del Señor.
Albarka ta tabbata ga waɗanda rayuwarsu ba ta da abin zargi, waɗanda suke tafiya bisa ga dokar Ubangiji.
2 Felices los que guardan sus mandamientos y con sinceridad desean seguirle.
Albarka ta tabbata ga waɗanda suke kiyaye ƙa’idodinsa suke kuma nemansa da dukan zuciyarsu.
3 Ellos no hacen el mal, y andan por su camino.
Ba sa yin wani abin da ba daidai ba; suna tafiya a hanyoyinsa.
4 Tú nos has ordenado seguir tus instrucciones con cuidado.
Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
5 ¡Deseo poder cumplir tus reglas de tal forma que puedas confiar en mi!
Kash, da a ce hanyoyina tsayayyu ne a yin biyayya da ƙa’idodinka mana!
6 Entonces no pasaré vergüenza cuando compare lo que hago con tus enseñanzas.
Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
7 Te alabaré con todo mi corazón porque de ti aprendo el modo correcto de vivir.
Zan yabe ka da zuciya ta gaskiya yayinda nake koyon dokokinka masu adalci.
8 Observaré tus leyes. ¡No me abandones nunca!
Zan yi biyayya da ƙa’idodinka; kada ka yashe ni ɗungum.
9 ¿Cómo puede un joven mantenerse puro? Siguiendo tus enseñanzas.
Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
10 Te alabo con todo mi corazón. No permitas que me aparte de tus mandamientos.
Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
11 En mi mente guardo tus enseñanzas para no pecar contra ti.
Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
12 ¡Gracias, Señor, por enseñarme lo que debo hacer!
Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
13 Repito en voz alta tus enseñanzas.
Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
14 Me deleito en tus enseñanzas más que en tener mucho dinero.
Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
15 Meditaré en tus enseñanzas con suma devoción, y reflexionaré sobre tus caminos.
Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
16 Me deleitaré en seguir tus mandamientos, y no olvidaré tus enseñanzas.
Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
17 Sé bondadoso con tu siervo para poder vivir y seguir tus enseñanzas.
Ka yi alheri ga bawanka, zan kuwa rayu; zan yi biyayya da maganarka.
18 Abre mis ojos para así poder entender las maravillas de tu ley.
Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
19 Sé que estoy aquí por poco tiempo. No permitas que pase por alto ninguna de tus enseñanzas.
Ni baƙo ne a duniya; kada ka ɓoye mini umarnanka.
20 Siempre deseo fervientemente saber tu voluntad.
Zuciyata ta ƙosa saboda marmari don dokokinka koyaushe.
21 Tú amonestas al arrogante, y quienes no siguen tus mandamientos son malditos.
Ka tsawata wa masu fariya, waɗanda suke la’anta waɗanda kuma suka kauce daga umarnanka.
22 No me dejes ser ridiculizado o recibir insultos, porque yo he guardado tus leyes.
Ka cire mini ba’a da reni, gama ina kiyaye farillanka.
23 Incluso los líderes se reúnen para calumniarme, pero yo, tu siervo, meditaré en tus enseñanzas con gran devoción.
Ko da yake masu mulki sun zauna tare suna ɓata mini suna, bawanka zai yi tunani a kan ƙa’idodinka.
24 Tus leyes me hacen feliz, pues son mis consejeras sabias.
Farillanka ne abin farin cikina; su ne mashawartana.
25 Muero aquí, tirado en el polvo. Mantenme con vida como me lo prometiste.
An kwantar da ni ƙasa cikin ƙura; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
26 Te expliqué mi situación y me respondiste. Enséñame a seguir tus instrucciones.
Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.
27 Ayúdame a entender el significado de tus leyes. Entonces meditaré en tus maravillas.
Bari in gane koyarwar farillanka; sa’an nan zan yi tunani a kan abubuwan banmamakinka.
28 Lloro porque tengo gran tristeza. Te pido que me consueles como me lo has prometido.
Raina ya gaji da baƙin ciki; ka ƙarfafa ni bisa ga maganarka.
29 Ayúdame a dejar de engañarme a mi mismo y enséñame tu ley con bondad.
Ka kiyaye ni daga hanyoyin ruɗu; ka yi mini alheri ta wurin dokokinka.
30 He elegido creer en ti y siempre estoy atento a tus enseñanzas.
Na zaɓi hanyar gaskiya; na sa zuciyata a kan dokokinka.
31 Guardo tus instrucciones, por eso te pido, Señor, que no me dejes quedar en ridículo.
Na riƙe farillanka kankan, ya Ubangiji; kada ka sa in sha kunya.
32 ¡Me apresuro a cumplir tus mandamientos, porque han abierto mi mente!
Ina gudu a kan hanyar umarnanka, gama ka’yantar da zuciyata.
33 Enséñame el significado de tus leyes y las seguiré siempre.
Ka koya mini Ya Ubangiji, don in bi ƙa’idodinka; sa’an nan zan kiyaye su har ƙarshe.
34 Ayúdame a entender para hacer tu voluntad con toda devoción.
Ka ba ni ganewa, zan kuwa kiyaye dokarka in kuma yi biyayya da ita da dukan zuciyata.
35 Guíame para que siga tus mandamientos, porque es lo que amo hacer.
Ka bi da ni a hanyar umarnanka, gama a can zan sami farin ciki.
36 Ayúdame a concentrarme en tus enseñanzas más que en obtener ganancias.
Ka juye zuciyata wajen farillanka ba wajen riba ta sonkai ba.
37 No me dejes poner mi mente en cosas vanas. Ayúdame a vivir en tus caminos.
Ka juye idanuna daga abubuwa marasa amfani; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
38 Por favor, mantén la promesa que me has hecho como tu siervo, y que has hecho a los que te adoran.
Ka cika alkawarinka ga bawanka, saboda a ji tsoronka.
39 Aleja la vergüenza que acarreo, porque tu ley es buena.
Ka kawar da shan kunyar da nake tsoro, gama dokokinka nagari ne.
40 Siempre deseo hacer tu voluntad. Por favor, déjame vivir porque tú eres justo.
Ina marmarin farillanka ƙwarai! Ka kiyaye raina cikin adalcinka.
41 Señor, por favor ámame con tu amor incondicional. Dame la salvación que me has prometido.
Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zo gare ni, ya Ubangiji, cetonka bisa ga alkawarinka;
42 Entonces podré responder a los que se burlan de mi, porque creo en tu palabra.
sa’an nan zan amsa wa masu cin mutuncina, gama na dogara ga maganarka.
43 No me impidas hablar tus palabras de verdad, porque he puesto toda mi confianza en tu justo juicio.
Kada ka ƙwace maganarka daga bakina, gama na sa zuciyata a dokokinka.
44 Seguiré viviendo tus enseñanzas por siempre y para siempre.
Kullayaumi zan yi biyayya da dokokinka, har abada abadin.
45 Viviré en libertad, porque me he dedicado a obedecerte.
Zan yi ta yawo a sake gama na nemi farillanka.
46 Instruiré a los reyes sobre tus leyes, y no seré avergonzado.
Zan yi maganar farillanka a gaban sarakuna ba kuwa za a kunyata ni ba,
47 Soy muy feliz de tener tus enseñanzas y las amo con todas mis fuerzas.
gama ina farin ciki da umarnanka saboda ina ƙaunarsu.
48 Elevo mis manos en oración, honrando tus mandamientos. Meditaré en tus enseñanzas con devoción.
Na ɗaga hannuwana ga umarnanka, waɗanda nake ƙauna, ina kuma tunani a kan ƙa’idodinka.
49 Recuerda la promesa que me has hecho, a mi, tu siervo. Tu promesa es mi única esperanza.
Tuna da maganarka ga bawanka, gama ka ba ni bege.
50 ¡En medio de mi miseria, solo me consuela tu promesa y me alienta a seguir!
Ta’aziyyata cikin wahalata ita ce alkawarinka yana kiyaye raina.
51 Los arrogantes se burlan de mi, pero yo no abandonaré tus enseñanzas.
Masu fariya suna yi mini ba’a ba tare da an hana su ba, amma ban rabu da dokar ba.
52 Medito en las instrucciones que nos diste hace mucho tiempo, Señor, y me proporcionan seguridad.
Na tuna da dokokinka na tun dā, ya Ubangiji, na kuwa sami ta’aziyya a cikinsu.
53 Me enojo con los malvados porque ellos han rechazado tu ley.
Fushi ya kama ni saboda mugaye, waɗanda suka keta dokokinka.
54 Tus enseñanzas son música a mis oídos en todo lugar donde habito.
Ƙa’idodinka su ne kan waƙata a duk inda na sauka.
55 Por la noche pienso en quien tú eres, Señor, y hago tu voluntad.
Da dare na tuna da sunanka, ya Ubangiji, zan kuwa kiyaye dokarka.
56 Porque vivo siguiendo tus principios.
Wannan shi ne na saba yi, ina yin biyayya da farillanka.
57 Señor, ¡tú eres mío! He prometido hacer tu voluntad.
Kai ne rabona, ya Ubangiji; na yi alkawarin in kiyaye maganarka.
58 Mi ser entero anhela tu bendición. Por favor, sé bondadoso conmigo, como me lo has prometido.
Na nemi fuskarka da dukan zuciyata; ka yi mini alheri bisa ga alkawarinka.
59 Al reflexionar sobre mi vida, vuelvo a decidir seguir tus enseñanzas.
Na lura da hanyoyina na kuma mayar da matakaina ga farillanka.
60 Me apresuro a cumplir tus mandamientos sin vacilar.
Zan gaggauta ba zan ɓata lokaci ba in yi biyayya da umarnanka.
61 Aún cuando los malvados traten de ponerme de su parte, no olvidaré tus enseñanzas.
Ko da yake mugaye sun ɗaura ni da igiyoyi, ba zan manta da dokokinka ba.
62 De noche despierto para agradecerte porque tu ley es buena.
Da tsakar dare nakan tashi in gode maka saboda dokokinka masu adalci.
63 Me agradan los que te siguen, los que hacen tu voluntad.
Ni aboki ne ga duk mai tsoronka, ga duk wanda yake bin farillanka.
64 Señor, tú amas a todos los habitantes de la tierra, pero a mi muéstrame tu voluntad.
Duniya ta cika da ƙaunarka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
65 Tú has sido muy bueno conmigo, Señor, tal como me lo has prometido.
Ka yi wa bawanka alheri bisa ga maganarka, ya Ubangiji.
66 Ahora enséñame a hacer juicio con justicia y a tener discernimiento porque creo en tus enseñanzas.
Ka koya mini sani da kuma hukunci mai kyau, gama na gaskata a umarnanka.
67 Antes estuve sufriendo, mientras vagaba lejos de ti, pero ahora hago tu voluntad.
Kafin in sha wahala na kauce, amma yanzu ina biyayya da maganarka.
68 Como eres bueno, todo lo que haces es bueno. Enséñame, Señor, tus caminos.
Kai nagari ne, kuma abin da kake yi yana da kyau; ka koya mini ƙa’idodinka.
69 Los arrogantes difaman mi reputación con mentiras, pero yo sigo tus mandamientos con todo mi corazón.
Ko da yake masu fariya sun shafe ni da ƙarairayi, na kiyaye farillanka da dukan zuciyata.
70 Ellos son fríos y e insensibles, pero yo amo tu ley.
Zukatansu sun yi tauri da kuma marasa tausayi amma ina farin ciki a dokarka.
71 El sufrimiento por el que pasé fue bueno para mi, porque pude meditar en lo que has dicho.
Ya yi kyau da na sha wahala don in koyi ƙa’idodinka.
72 Tus enseñanzas son más valiosas para mi que el oro y la plata en abundancia.
Doka daga bakinka ya fi mini daraja fiye da azurfa da zinariya guda dubu.
73 Tú me creaste y me hiciste como soy. Ayúdame a entender mejor tus mandamientos.
Hannuwanka ne suka yi suka kuma siffanta ni; ka ba ni ganewa don in koyi umarnanka.
74 Que los que te adoran se alegren al verme, porque he puesto mi confianza en tu palabra.
Bari waɗanda suke tsoronka su yi farin ciki sa’ad da suke gan ni, gama na sa zuciyata a maganarka.
75 Señor, yo sé que decides con rectitud. Tú me derribaste para ayudarme porque eres fiel.
Ya Ubangiji na sani, cewa dokokinka masu adalci ne, kuma cikin aminci ka hore ni.
76 Te pido que tu amor y fidelidad me consuelen como me lo has prometido.
Bari ƙaunarka marar ƙarewa tă yi mini ta’aziyya, bisa ga alkawarinka ga bawanka.
77 Ten compasión de mi para que pueda vivir, porque amo tus enseñanzas.
Bari tausayinka yă zo mini don in rayu, gama dokarka ce farin cikina.
78 Derriba a los orgullosos que me han hecho daño con sus mentiras. Yo me dedicaré a meditar en tus enseñanzas.
Bari masu girman kai su sha kunya saboda abubuwa marasa kyau da suke yi mini ba dalili; amma zan yi tunani a kan farillanka.
79 Permite que los que te siguen me busquen, aquellos que entienden tus leyes.
Bari waɗanda suke tsoronka su juya gare ni, waɗanda suka gane da farillanka.
80 Que en mi inocencia pueda seguir tus normas sin ser avergonzado.
Bari zuciyata ta kasance marar abin zargi wajen ƙa’idodinka, don kada in sha kunya.
81 Me siento agotado de tanto esperar por tu salvación, pero mantengo mi esperanza en tu palabra.
Raina ya tafke da marmari don cetonka, amma na sa zuciyata a maganarka.
82 Mis ojos se esfuerzan por guardar tus promesas, y se preguntan cuándo vendrás a consolarme.
Idanuna sun gaji, suna jiran alkawarinka; Na ce, “Yaushe za ka ta’azantar da ni?”
83 Estoy arrugado como un odre arrugado por el humo. Pero no he olvidado cómo hacer tu voluntad.
Ko da yake ni kamar salkar ruwan inabi ne a cikin hayaƙi, ban manta da ƙa’idodinka ba.
84 ¿Hasta cuándo tengo que esperar para que castigues a mis perseguidores?
Har yaushe bawanka zai yi ta jira? Yaushe za ka hukunta masu tsananta mini?
85 Estas personas arrogantes han cavado huecos para hacerme caer. No conocen tu ley.
Masu girman kai sun haƙa mini rami, sun ƙetare dokarka.
86 Todos tus mandamientos son fieles. Ayúdame para mantenerme en pie ante estas personas que me persiguen con sus mentiras.
Dukan umarnanka abin dogara ne; ka taimake ni, gama mutane suna tsananta mini ba dalili.
87 Casi me han matado, pero no he dejado de hacer tu voluntad.
Sun kusa gama da ni a duniya, amma ban bar bin farillanka ba.
88 Por tu amor incondicional, Señor, no me dejes morir, para poder seguir andando según las enseñanzas que me has dado.
Ka kiyaye raina bisa ga ƙaunarka, zan kuwa yi biyayya da farillan bakinka.
89 Señor, tu palabra permanece para siempre, y se mantiene firme en los cielos.
Maganarka, ya Ubangiji madawwamiya ce; tana nan daram a cikin sammai.
90 Tu fidelidad se extiende por generaciones, y es tan permanente como la tierra que tú creaste.
Amincinka yana cin gaba cikin dukan zamanai; ka kafa duniya ta kuma dawwama.
91 Tus juicios siguen vigentes —aun hasta hoy—porque todo sirve a tu voluntad.
Dokokinka sun dawwama har yă zuwa yau, gama dukan abubuwa suna maka hidima.
92 Si no fuera porque amo tus enseñanzas, mi sufrimiento me habría matado.
Da ba don dokarka ce farin cikina ba, da na hallaka a cikin azabana.
93 Nunca olvidaré tus instrucciones, porque a través de ellas me das vida.
Ba zan taɓa manta da farillanka ba, gama ta wurinsu ne ka kiyaye raina.
94 Soy tuyo, Señor. ¡Sálvame! Sabes que con devoción sigo tus principios.
Ka cece ni, gama ni naka ne; na yi ƙoƙarin neman farillanka.
95 Aunque los malvados están esperando para tomarme por sorpresa y matarme, mantendré mi pensamiento enfocado en tus enseñanzas.
Mugaye suna jira su hallaka ni, amma zan yi ta tunani a kan farillanka.
96 Reconozco que la perfección humana tiene límites, pero tus leyes no tienen límites.
Ga duk cikakke na ga kāsawa; amma umarnanka ba su da iyaka.
97 ¡Cuánto amo tu ley! En ella medito de día y de noche.
Kash, ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina tunani a kanta dukan yini.
98 Tus mandamientos me han hecho más sabio que mis enemigos, porque siempre estoy pensando en tus instrucciones.
Umarnanka suna sa in zama mai hikima fiye da abokan gābana, gama kullum suna tare da ni.
99 De hecho, he adquirido mayor entendimiento que todos mis maestros, porque dedico mi tiempo a meditar en tus enseñanzas.
Ina da ganewa sosai fiye da dukan malamaina, gama ina tunani a kan farillanka.
100 Hasta mi entendimiento supera al de los ancianos, porque sigo tus caminos.
Ina da ganewa fiye da dattawa, gama ina biyayya da farillanka.
101 Evito hacer cualquier cosa que conduzca al mal, porque quiero seguir fiel a tu palabra.
Na kiyaye ƙafafuna daga kowace muguwar hanya domin in yi biyayya da maganarka.
102 Nunca he rechazado tus enseñanzas porque tu mismo me has enseñado lo que debo hacer.
Ban rabu da dokokinka ba, gama kai da kanka ne ka koya mini.
103 Tus palabras son dulces para mi. Más dulces que la miel en mi boca.
Ɗanɗanon maganarka akwai zaki, sun ma fi zuma zaki a bakina!
104 Mi entendimiento aumenta al escuchar tu palabra. Por ello aborrezco los caminos del engaño.
Na sami ganewa daga farillanka; saboda haka ina ƙin kowace hanyar da ba daidai ba.
105 Tu palabra es una lámpara que me muestra por dónde caminar. Y es una luz en mi camino.
Maganarka fitila ce ga ƙafafuna haske kuma a kan hanyata.
106 ¡He hecho una promesa, y la mantendré! ¡Seguiré tus principios porque son rectos!
Na yi rantsuwa na kuma tabbatar da shi, cewa zan bi dokokinka masu adalci.
107 ¡Señor, mira cuánto estoy sufriendo! Por favor, déjame vivir, tal como me lo has prometido.
Na sha wahala sosai; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga maganarka.
108 Por favor, Señor, acepta mi ofrenda de adoración que te traigo de todo corazón. Enséñame tus principios.
Ka karɓi yabon bakina da nake yi da yardar rai, ya Ubangiji, ka kuwa koya mini dokokinka.
109 Mi vida siempre está en peligro, pero nunca me olvidaré de tu ley.
Ko da yake kullum ina riƙe da raina a hannuwana, ba zan manta da dokarka ba.
110 Los malvados me han tendido trampas, pero no me alejaré de tus mandamientos.
Mugaye sun kafa mini tarko, amma ban kauce daga farillanka ba.
111 Siempre me aferraré a tus enseñanzas porque tu palabra me llena de felicidad.
Farillanka su ne gādona har abada; su ne farin cikin zuciyata.
112 He decidido seguir tus enseñanzas hasta el final.
Zuciyata ta shirya a kan kiyaye ƙa’idodinka har ƙarshe.
113 Aborrezco a los hipócritas pero amo tu ley.
Na ƙi mutane masu baki biyu, amma ina ƙauna dokarka.
114 Tú me mantienes a salvo y me defiendes. Tu palabra alimenta mi esperanza.
Kai ne mafakata da garkuwata; na sa zuciyata a maganarka.
115 Déjenme en paz, hombres malvados. Déjenme seguir los mandamientos de mi Dios.
Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta, don in kiyaye umarnan Allahna!
116 Sé mi sostén, Señor, como me lo has prometido, para poder seguir viviendo. No dejes que mi esperanza se convierta en desánimo.
Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.
117 Sé mi consuelo, para ser salvo y seguir atendiendo tus enseñanzas.
Ka riƙe ni za a kuma cece ni; kullayaumi zan ɗauka ƙa’idodinka da muhimmanci.
118 Tú aborreces a los que no te obedecen. Ellos se engañan a sí mismos con una vida de mentiras.
Ka ki dukan waɗanda suka kauce daga ƙa’idodinka, gama yaudararsu banza ne.
119 Tú tratas a los perversos en la tierra como seres despreciables que han de ser desechados. Por eso amo tu ley.
Dukan mugayen duniya ka zubar kamar datti; saboda haka nake ƙaunar farillanka.
120 ¡Me estremezco al pensar en ti, y te temo por tus juicios!
Naman jikina na rawan jiki don tsoronka; na cika da tsoron dokokinka.
121 He hecho lo justo y lo recto. Por ello, no me abandones en manos de mis enemigos.
Na aikata abin da yake mai adalci da kuma daidai; kada ka ni a hannun masu danne ni.
122 Por favor, prométeme que cuidarás de mi tu siervo. No dejes que los arrogantes me maltraten.
Ka tabbatar da lafiyar bawanka; kada ka bar masu girman kai su danne ni.
123 Mis ojos están cansados de esperar tu salvación, tratando de ver cumplida tu promesa de hacer buenas todas las cosas.
Idanuna sun gaji, da jiran cetonka, da jiran alkawarinka mai adalci.
124 A mi, que soy tu siervo, trátame según tu amor y fidelidad. Enséñame tu voluntad.
Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
125 Soy tu siervo. Por favor, dame discernimiento para entender tus enseñanzas.
Ni bawanka ne, ka ba ni fahimi don in gane farillanka.
126 Señor, ya es hora de que actúes respecto a estas personas que han quebrantado tus leyes.
Lokaci ya yi da za ka yi wani abu, ya Ubangiji; ana karya dokarka.
127 Por ello amo tus mandamientos más que el oro. Más que el oro puro.
Saboda ina ƙaunar umarnanka fiye da zinariya, kai, fiye da zinariya zalla,
128 Cada uno de tus principios es justo. Por ello aborrezco los caminos del engaño.
saboda kuma ina lura da dukan farillanka da kyau, na ƙi kowace hanyar da ba daidai ba.
129 ¡Tus leyes son maravillosas y por ello las obedezco!
Farillanka masu banmamaki ne; saboda haka nake yin biyayya da su.
130 El estudiar tu palabra proporciona tanta luz, que aún los iletrados pueden etenderla.
Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.
131 Anhelo con fervor escuchar tu voluntad.
Ina hakkin da bakina a buɗe, ina marmarin umarnanka.
132 Por favor, escúchame y sé bondadoso conmigo, como lo eres con todos los que te aman.
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, yadda kullum ka yi wa waɗanda suke ƙaunar sunanka.
133 Muéstrame a través de tu palabra el camino que debo tomar, y no dejes que ningún mal se apodere de mi.
Ka bi da sawuna bisa ga maganarka; kada ka bar zunubi yă mallake ni.
134 Sálvame de la gente cruel, para poder seguir tus enseñanzas.
Ka fanshe ni daga mutane masu danniya, don in yi biyayya da farillanka.
135 Por favor, mírame con amor, a mi, tu siervo; y enséñame lo que debo hacer.
Ka sa fuskarka ta haskaka a kan bawanka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
136 Mis lágrimas corren por mi rostro mientras lloro por los que no guardan tu ley.
Hawaye suna malalowa daga idanuna kamar rafi, gama ba a biyayya da dokarka.
137 ¡Señor, tú eres recto y tus decisiones son justas!
Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
138 Tú me has dado tus mandatos que son justos y absolutamente confiables.
Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
139 Mi devoción me consume porque mis enemigos ignoran tu palabra.
Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
140 Tus promesas se han cumplido, y por ello, yo, tu siervo, las amo.
An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
141 Quizás soy insignificante y despreciado, pero nunca me olvido de tus mandamientos.
Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
142 Tu bondad y tu justicia duran para siempre. Tu ley es la verdad.
Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
143 Cuando estoy triste y en problemas, tus mandamientos me llenan de felicidad.
Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
144 Tus leyes siempre son justas. Ayúdame a entenderlas para poder vivir.
Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
145 ¡Mi ser entero clama a ti, Señor! ¡Por favor, respóndeme! Yo seguiré tus mandatos.
Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
146 A ti oro, y pido salvación para poder hacer tu voluntad.
Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
147 Temprano me levanto y clamo a ti por ayuda. En tu palabra pongo mi esperanza.
Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
148 En la noche hago vigilia y medito en tu palabra.
Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
149 Escúchame, Señor, con amor incondicional. Guarda mi vida, Señor, porque siempre haces lo recto.
Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
150 Los malvados se apresuran a atacarme. Ellos rechazan por tu palabra por completo.
Waɗanda suke ƙirƙiro mugayen dabaru suna nan kusa, amma suna nesa da dokarka.
151 Pero tú, Señor, estás aquí a mi lado. Todos tus mandamientos son verdaderos.
Duk da haka kana kusa, ya Ubangiji, kuma dukan umarnanka gaskiya ne.
152 Desde hace mucho entendí que tus leyes permanecerán para siempre.
Tun tuni na koyi daga farillanka cewa ka kafa su su kasance har abada.
153 ¡Por favor mira mi sufrimiento y sálvame! Mira que no me he olvidado de tus enseñanzas.
Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.
154 Defiende mi causa y sálvame conforme a tu promesa. ¡Guarda mi vida, Señor!
Ka kāre manufata ka kuma fanshe ni, ka cece rai na kamar yadda ka alkawarta!
155 Los malvados no pueden ser salvos, porque menosprecian tus enseñanzas.
Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa neman ƙa’idodinka.
156 ¡Pero Señor, tu misericordia es grande! ¡Te pido que por tu justicia me dejes vivir!
Tausayinka da girma yake, ya Ubangiji; ka kiyaye raina bisa ga dokokinka.
157 A pesar de que muchos me maltratan y me persiguen, no me he apartado de tu ley.
Maƙiya masu yawa ne suke tsananta mini, amma ban rabu da farillanka ba.
158 Me indigna ver a los infieles porque aborrecen tu palabra.
Na dubi marasa aminci da ƙyama, gama ba sa yin biyayya da maganarka.
159 Señor, mira cuánto amo tus mandamientos. Por favor, déjame vivir, conforme a tu amor incondicional.
Dubi yadda nake ƙaunar farillanka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga ƙaunarka.
160 ¡Tu palabra es verdad! Y todas tus leyes permanecerán para siempre.
Dukan maganganunka gaskiya ne; dukan dokokinka masu adalci madawwami ne.
161 Los líderes me persiguen sin razón alguna, pero yo solo respeto a tu palabra.
Masu mulki suna tsananta mini ba dalili, amma zuciyata na rawan jiki game da maganarka.
162 Tu palabra me hace tan feliz como aquél que encuentra un inmenso tesoro.
Ina farin ciki da alkawarinka kamar yadda wani kan sami ganima mai girma.
163 Aborrezco y rechazo la mentira, pero amo tus enseñanzas.
Na ƙi ina kuma ƙyamar ƙarya amma ina ƙaunar dokarka.
164 Te alabo siete veces al día porque tus leyes son buenas.
Sau bakwai a rana ina yabonka saboda dokokinka masu adalci.
165 Los que aman tus enseñanzas viven en paz y nada los hace caer.
Waɗanda suke ƙaunar dokarka suna da babban salama, kuma babu abin da zai sa su yi tuntuɓe.
166 Señor, espero con ansias tu salvación y guardo tus mandamientos.
Ina jiran cetonka, ya Ubangiji, ina kuma bin umarnanka.
167 Obedezco tus leyes y las amo con todo mi corazón.
Ina biyayya da farillanka, gama ina ƙaunarsu ƙwarai.
168 Guardo tus mandamientos y tus leyes porque tú ves todo lo que hago.
Ina biyayya da farillanka da kuma koyarwarka, gama dukan hanyoyina sanannu ne gare ka.
169 Señor, escucha mi triste lamento. Ayúdame a entender conforme me lo has prometido.
Bari kukata ta zo gare ka, ya Ubangiji; ka ba ni ganewa bisa ga maganarka.
170 Por favor, escúchame y sálvame confirme a tu promesa.
Bari roƙona yă zo gabanka; ka cece ni bisa ga alkawarinka.
171 Déjame elevar alabanzas a ti, porque tú me enseñas lo que debo hacer.
Bari leɓunana su cika da yabonka, gama ka koya mini ƙa’idodinka.
172 Cantaré de tu palabra, porque todos tus mandamientos son rectos.
Bari harshena yă rera game da maganarka, gama dukan umarnanka masu adalci ne.
173 Por favor, sé pronto para ayudarme porque he elegido seguir tus caminos.
Bari hannunka yă kasance a shirye don yă taimake ni, gama na zaɓi farillanka.
174 Anhelo tu salvación, Señor; y tus enseñanzas me proporcionan felicidad.
Ina marmarin cetonka, ya Ubangiji, dokarka kuwa ita ce farin cikina.
175 Ojalá pueda vivir alabándote y que tus enseñanzas sean mi ayuda.
Bari in rayu don in yabe ka, bari kuma dokokinka su raya ni.
176 He vagado como una oveja perdida; por eso te pido que vengas a buscarme, porque no me he olvidado de tus mandamientos.
Na kauce kamar ɓatacciyar tunkiya. Ka nemi bawanka, gama ban manta da umarnanka ba.

< Salmos 119 >