< Salmos 115 >

1 No para nosotros, Señor, no para nosotros, sino para ti Señor, toda la gloria debe ser dada, por tu gran amor y verdad.
Ba gare mu ba, ya Ubangiji, ba gare mu ba amma ga sunanka yă sami ɗaukaka, saboda ƙaunarka da amincinka.
2 Por qué deberían las naciones paganas preguntar, “¿Dónde está tu Dios?”
Me ya sa al’ummai suke cewa, “Ina Allahnsu?”
3 Nuestro Dios está en el cielo, y Él hace lo que quiere.
Allahnmu yana a sama; yana yin duk abin da ya ga dama.
4 Sus ídolos son solo objetos hechos de plata y de oro por manos humanas.
Amma gumakansu azurfa da zinariya ne, da hannuwan mutane suka yi.
5 Tienen bocas, pero no pueden hablar. Tienen ojos, pero no pueden ver.
Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
6 Tienen oídos, pero no pueden oír. Tienen narices, pero no pueden oler.
suna da kunnuwa, amma ba sa ji, hanci, amma ba sa jin ƙanshi
7 Tienen manos, pero no pueden sentir. Tienen pies, pero no pueden caminar. Ni un solo sonido viene de sus gargantas.
suna da hannuwa, amma ba sa iya taɓa kome, ƙafafu, amma ba sa iya tafiya; ba sa iya ce wani abu da maƙogwaronsu.
8 Todos los que hacen ídolos se vuelven como ellos, y también pasa esto con los confían en ellos.
Masu yinsu za su zama kamar su, haka kuma zai kasance da duk wanda ya dogara da su.
9 Israel, ¡Confía en el Señor! Él es el único que te ayuda y te protege.
Ya gidan Isra’ila, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
10 Descendientes de Aarón, ¡confíen en el Señor! Él es el único que los protege y los ayuda.
Ya gidan Haruna, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
11 Aquellos que honran al Señor, ¡Confíen en el Señor! Él es el único que los protege y los salva.
Ku da kuke tsoronsa, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
12 El Señor nos recordará y será bueno con nosotros. Él bendecirá a Israel, bendecirá a los descendientes de Aarón.
Ubangiji yakan tuna da mu zai kuma albarkace mu. Zai albarkace gidan Isra’ila, zai albarkace gidan Haruna,
13 El Señor bendecirá a todos los que lo adoran, quienesquiera que sean.
zai albarkace waɗanda suke tsoron Ubangiji, manya da ƙanana duka.
14 Que el Señor sea bueno contigo, contigo y con tus hijos.
Bari Ubangiji yă sa ku ƙaru, da ku da’ya’yanku.
15 Que seas bendecido por el Señor que hizo los cielos y la tierra.
Bari Ubangiji yă albarkace ku, shi Mahalicci sama da ƙasa.
16 Los cielos pertenecen al Señor, pero él le ha dado la tierra a la humanidad.
Saman sammai na Ubangiji ne, amma ya ba da duniya ga mutum.
17 La muerte no alaba al Señor, ni ninguno de aquellos que han descendido al silencio de la tumba
Ba matattu ba ne masu yabon Ubangiji, waɗanda suke gangara zuwa wurin da ake shiru;
18 Pero nosotros, los que estamos vivos alabaremos al Señor desde ahora y para siempre. ¡Alaben al Señor!
mu ne masu ɗaukaka Ubangiji, yanzu da har abada kuma. Yabi Ubangiji.

< Salmos 115 >