< Salmos 107 >

1 ¡Agradezcan al Señor, porque él es bueno! ¡Su misericordioso amor perdura para siempre!
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Que todos a los que salvó salgan a gritarle al mundo; aquellos a quienes rescató del poder del enemigo.
Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
3 Los ha reunido desde tierras lejanas, desde el este y el oeste, y del norte y el sur.
su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
4 Ellos vagaron por el árido desierto, sin encontrar una sola ciudad en la que vivir.
Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
5 Hambrientos y sedientos, se desanimaron.
Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
6 Entonces clamaron al Señor para que los ayudara, y los salvó de su sufrimiento.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
7 Los guió por un camino directo a la ciudad donde podrían vivir.
Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
8 Alaben al Señor por su gran amor, y por todas las cosas hermosas que hace por la gente.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
9 Porque brinda agua al sediento, y alimenta a los hambrientos.
gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
10 Algunos se sientan en completas tinieblas, prisioneros de la miseria y atados con cadenas de hierro,
Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
11 Porque se han revelado contra lo que Dios ha dicho; han rechazado la dirección del Altísimo.
gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
12 Entonces Dios humillará su orgullo con los problemas de la vida; tropezarán y no habrá nadie cerca que los ayude a no caer.
Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
13 Y llamarán al Señor en medio de sus problemas, y los salvará de su sufrimiento.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
14 Los traerá de vuelta desde las tinieblas, romperá en pedazos sus cadenas.
Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
15 Alaben al Señor por su gran amor, y por todas las cosas hermosas que hace por la gente.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
16 Porque Él rompe las puertas de bronce, y corta las barras de hierro.
gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
17 Ellos fueron necios al rebelarse; y sufrieron por sus pecados.
Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
18 No quisieron comer; y estuvieron a las puertas de la muerte.
Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
19 Entonces llamaron al Señor para que los ayudara, y Él los salvó de su sufrimiento.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
20 Dio la orden y fueron sanados; los salvó de la tumba.
Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
21 Alaben al Señor por su gran amor, y por todas las cosas hermosas que hace por la gente.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
22 Preséntense ante él con ofrendas de gratitud y canten de alegría sobre lo que ha hecho.
Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
23 Los que zarpan en barcos, y cruzan océanos para ganar la vida,
Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
24 ellos han visto el increíble poder de Dios en marcha, y las maravillas que hizo en aguas profundas.
Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
25 Él solo tiene que hablar para causar vientos tormentosos y levantar grandes olas,
Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
26 Lanzando a los barcos al aire y luego arrastrándolos una vez más al suelo. Los navegantes estaban tan aterrorizados que su coraje se desvaneció.
Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
27 Se tambalearon, cayendo de lado a lado como ebrios, todas sus habilidades de marineros les fueron inútiles.
Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
28 Entonces llamaron al Señor para que los ayudara, y Él los salvó de su sufrimiento.
Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
29 Calmó la tempestad, y las olas se aquietaron.
Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
30 Los navegantes estaban tan felices de que las aguas se hubieran calmado, y el Señor los llevó hasta el puerto que querían.
Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
31 Alaben al Señor por su gran amor, y por todas las cosas hermosas que ha hecho por su pueblo.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
32 Digan cuán maravilloso es en frente de toda la congregación y de los ancianos.
Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
33 Él seca ríos y convierte tierras en desiertos; las cascadas de agua dejan de fluir y la tierra se vuelve seca y polvorienta.
Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
34 Los terrenos fructíferos se convierten tierras arenosas y baldías a causa de la maldad de los que allí vivían.
ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
35 Pero Él también se vuelve y hace lagunas de agua en mitad del desierto, y hace fluir cascadas en tierras secas.
Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
36 Trae a la gente hambrienta a un lugar donde pueden reconstruir sus ciudades.
a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
37 Ellos siembran sus campos y plantan viñas, produciendo buena cosecha.
Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
38 Él cuida de su pueblo, y este aumenta su tamaño drásticamente, también el número de sus ganados!
ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
39 Cuando son pocos, reducidos por el dolor, la miseria y la opresión.
Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
40 Derrama su desprecio hacia sus líderes, haciéndolos vagar, perdidos en el desierto.
shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
41 Pero Él saca al pobre de sus problemas, y hace a sus familias tan grandes como los rebaños.
Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
42 Los que viven en rectitud mirarán lo que está pasando y se alegrarán, pero los malvados serán silenciados.
Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
43 Aquellos que son sabios prestarán atención a esto, y meditarán en el gran amor de Dios.
Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.

< Salmos 107 >