< Proverbios 3 >

1 Hijo mío, no olvides mis instrucciones. Recuerda siempre mis mandamientos.
Ɗana, kada ka manta da koyarwata, amma ka kiyaye umarnaina a cikin zuciyarka,
2 Así vivirás muchos años, y tu vida será plena.
gama za su ƙara maka tsawon rai da shekaru masu yawa su kuma kawo maka wadata.
3 Aférrate a la bondad y a la verdad. Átalas a tu cuello y escríbelas en tu mente.
Kada ka bar ƙauna da aminci su rabu da kai; ka ɗaura su kewaye da wuyanka, ka rubuta su a allon zuciyarka.
4 Así tendrás buena reputación y serás apreciado por Dios y la gente.
Sa’an nan za ka sami tagomashi da kuma suna mai kyau a gaban Allah da kuma a gaban mutane.
5 Pon tu confianza totalmente en el Señor, y no te fíes de lo que crees saber.
Ka dogara ga Ubangiji da dukan zuciyarka kada kuma ka dangana ga ganewarka;
6 Recuérdalo en todo lo que hagas, y él te mostrará el camino correcto.
cikin dukan hanyoyinka ka amince da shi, zai kuwa sa hanyoyinka su miƙe.
7 No te creas sabio, respeta a Dios y evita el mal.
Kada ka zama mai hikima a ganinka; ka ji tsoron Ubangiji ka kuma guji mugunta.
8 Entonces serás sanado y fortalecido.
Wannan zai ba wa jikinka lafiya yă kuma adana ƙasusuwanka.
9 Honra al Señor con tu riqueza y con los primeros frutos de tus cosechas.
Ka girmama Ubangiji da dukan dukiyarka, ta wurin miƙa masa nunan fari na dukan amfanin gonarka;
10 Entonces tus graneros serán llenos de fruto, y tus estanques rebosarán de vino nuevo.
ta haka rumbunanka za su cika har su zuba, randunanka kuma su cika har baki da sabon ruwan inabi.
11 Hijo mío, no rechaces la disciplina del Señor ni te enojes cuando te corrija,
Ɗana, kada ka rena horon Ubangiji kada kuma ka ƙi tsawatawarsa,
12 porque el Señor corrige a los que ama, así como un padre corrige al hijo que más le agrada.
domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, kamar yadda mahaifi yake yin wa ɗa da yake fariya da shi.
13 Felices son los que encuentran la sabiduría y obtienen entendimiento,
Mai albarka ne mutumin da ya sami hikima, mutumin da ya sami fahimi,
14 porque la sabiduría vale más que la plata, y ofrece mejor recompensa que el oro.
gama ta fi azurfa riba tana kuma da amfani fiye da zinariya.
15 ¡La sabiduría vale más que muchos rubíes y no se compara con ninguna cosa que puedas imaginar!
Ta fi lu’ulu’u daraja; ba a kwatanta abin da ka fi sha’awa da ita.
16 Por un lado ella te brinda larga vida, y por el otro riquezas y honra.
Tsawon rai yana a cikin hannunta na dama; a hannunta na hagu kuwa akwai arziki da bangirma.
17 Te dará verdadera felicidad, y te guiará a una prosperidad llena de paz.
Hanyoyinta hanyoyi ne masu daɗi, dukan hanyoyinta kuma salama ne.
18 La sabiduría es un árbol de vida para todo el que se aferra a ella, y bendice a todos los que la aceptan.
Ita itacen rai ne ga waɗanda suka rungume ta; waɗanda suke riƙe da ta za su zama masu albarka.
19 Fue gracias a la sabiduría el Señor creó la tierra, y gracias al conocimiento puso los cielos en su lugar.
Ta wurin hikima Ubangiji ya kafa harsashin duniya, ta wurin fahimi ya shirya sammai inda suke;
20 Fue gracias a su conocimiento que las aguas de las profundidades fueron liberadas, y las nubes enviadas como rocío.
ta wurin sani aka rarraba zurfafa, gizagizai kuma suka zubo raɓa.
21 Hijo mío, aférrate al buen juicio y a las decisiones sabias; no los pierdas de vista,
Ɗana, ka riƙe sahihiyar shari’a da kuma basira, kada ka bar su su rabu da kai;
22 porque serán vida para ti, y como un adorno en tu cuello.
za su zama rai a gare ka, abin adon da zai gyara wuyanka.
23 Caminarás con confianza y no tropezarás.
Sa’an nan za ka bi hanyarka lafiya, ƙafarka kuwa ba zai yi tuntuɓe ba;
24 Cuando descanses, no tendrás temor, y cuando te acuestes tu sueño será placentero.
sa’ad da ka kwanta, ba za ka ji tsoro ba; sa’ad da ka kwanta, barci zai yi maka daɗi.
25 No tendrás temor del pánico repentino, ni de los desastres que azotan al malvado,
Kada ka ji tsoron masifar da za tă faru farat ɗaya ko lalacin da yakan auka wa mugaye,
26 porque el Señor será tu confianza, y evitará que caigas en trampa alguna.
gama Ubangiji zai zama ƙarfin halinka zai kuwa kiyaye ƙafarka daga fāɗawa a tarko.
27 No le niegues el bien a quien lo merece cuando tengas el poder en tus manos.
Kada ka ƙi yin alheri ga duk wanda ya dace, sa’ad da kana iya yin haka.
28 No le digas a tu prójimo: “Vete. Ven mañana, y yo te daré”, si ya tienes los recursos para darle.
Kada ka ce wa maƙwabcinka “Ka yă dakata sai gobe,” idan kana iya taimakonsa yanzu.
29 No hagas planes para perjudicar a tu prójimo que vive junto a ti, y que confía en ti.
Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka, wanda yake zama da aminci kusa da kai.
30 No discutas con nadie sin razón, si no han hecho nada para hacerte daño alguno.
Kada ka zargi mutum ba dalili, sa’ad da bai yi laifi ba.
31 ¡No sientas celos de los violentos, ni sigas su ejemplo!
Kada ka ji kishin mai tā-da-na-zaune-tsaye ko ka yi sha’awar aikata ayyukansu.
32 Porque el Señor aborrece a los mentirosos, pero es amigo de los que hacen lo que es bueno.
Gama Ubangiji yana ƙyama mai aikata mugunta amma yakan rungumi adalin da ya amince da shi.
33 Las casas de los malvados están malditas por el Señor, pero él bendice los hogares de los que viven en rectitud.
La’anar Ubangiji tana a gidan mugaye, amma yakan albarkaci gidan adali.
34 Él se burla de los que se burlan, pero es bondadoso con los humildes.
Yakan yi wa masu girman kai ba’a amma yakan yi wa mai sauƙinkai alheri.
35 Los sabios recibirán honra, pero los necios permanecerán en desgracia.
Masu hikima sukan sami kyakkyawan suna, amma wawaye sukan ƙara wa kansu shan kunya.

< Proverbios 3 >