< Nehemías 7 >

1 Una vez reconstruida la muralla y levantadas las puertas, nombré a los porteros, a los cantores y a los levitas.
Bayan an sāke gina katangar na kuma sa ƙofofi a wurarensu, sai aka naɗa masu tsaro, da mawaƙa, da Lawiyawa.
2 Puse a mi hermano Hanani a cargo de Jerusalén, junto con Hananías, el comandante de la fortaleza, porque era un hombre honesto que respetaba a Dios más que muchos otros.
Na sa ɗan’uwana Hanani tare da Hananiya shugaban fada aikin riƙon Urushalima, domin shi Hananiya mutum mai mutunci ne, mai tsoron Allah fiye da yawancin mutane.
3 Les dije: “No permitan que se abran las puertas de Jerusalén hasta que el sol esté caliente, y asegúrate de que los guardias cierren y echen el cerrojo a las puertas mientras estén de servicio. Nombra a algunos de los habitantes de Jerusalén como guardias, para que estén en sus puestos, frente a sus propias casas”.
Na ce musu, “Kada a buɗe ƙofofin Urushalima da sassafe sai rana ta fito sosai. Yayinda matsaran ƙofofi suna aiki, a kulle ƙofofin a sa musu sakata kafin matsaran su tashi, wajen fāɗuwar rana. Ku kuma naɗa mazaunan Urushalima a matsayin masu tsaro, waɗansunsu a wuraren aiki, waɗansun kuma kusa da gidajensu.”
4 En aquellos tiempos la ciudad era grande y con mucho espacio, pero no había mucha gente en ella, y las casas no habían sido reconstruidas.
Birnin Urushalima kuwa tana da fāɗi da girma, amma mutanen da suke zama a cikinta kaɗan ne, ba a kuma gina gidaje da yawa ba tukuna.
5 Mi Dios me animó a que todos -los nobles, los funcionarios y el pueblo- vinieran a registrarse según su genealogía familiar. Encontré el registro genealógico de los que habían regresado primero. Esto es lo que descubrí escrito allí.
Sai Allahna ya sa a zuciyata in tara manyan gari, shugabanni da talakawa don a rubuta su bisa ga iyalansu. Na sami littafin asali na waɗanda suka fara dawowa. Ga abin da na tarar an rubuta a ciki.
6 Esta es una lista de la gente de la provincia que regresó del cautiverio. Estos eran los exiliados que habían sido llevados a Babilonia por el rey Nabucodonosor. Regresaron a Jerusalén y a Judá, a sus ciudades de origen.
Waɗannan su ne mutanen yankin da suka dawo daga zaman bautar da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kame (sun dawo Urushalima da Yahuda, kowanne zuwa garinsa.
7 Estaban dirigidos por Zorobabel, Jesúa, Nehemías, Azarías, Raamías, Nahamani, Mardoqueo, Bilsán, Misperet, Bigvai, Nehum y Baana. Este es el número de hombres del pueblo de Israel:
Sun dawo tare da Zerubbabel, da Yeshuwa, da Nehemiya, da Azariya, da Ra’amiya, da Nahamani, da Mordekai, da Bilshan, da Misfar, da Bigwai, da Nehum da kuma Ba’ana). Ga jerin mutanen Isra’ila.
8 Los hijos de Paros, 2.172;
Zuriyar Farosh mutum 2,172
9 los hijos de Sefatías, 372;
ta Shefatiya 372
10 los hijos de Ara, 652;
ta Ara 652
11 los hijos de Pahat-moab, (los hijos de Jesúa y Joab), 2.818;
ta Fahat-Mowab (ta wurin Yeshuwa da Yowab) 2,818
12 los hijos de Elam, 1.254;
ta Elam 1,254
13 los hijos de Zatu, 845;
ta Zattu 845
14 los hijos de Zacai, 760;
ta Zakkai 760
15 los hijos de Binui, 648;
ta Binnuyi 648
16 los hijos de Bebai, 628;
ta Bebai 628
17 los hijos de Azgad, 2.322;
ta Azgad 2,322
18 los hijos de Adonicam, 667;
ta Adonikam 667
19 los hijos de Bigvai, 2.067.
ta Bigwai 2,067
20 Los hijos de Adin, 655.
ta Adin 655
21 Los hijos de Ater, (hijos de Ezequías), 98;
ta Ater (ta wurin Hezekiya) 98
22 los hijos de Hasum, 328;
ta Hashum 328
23 los hijos de Bezai, 324;
ta Bezai 324
24 los hijos de Harif, 112;
ta Harif 112
25 los hijos de Gabaón, 95;
ta Gibeyon 95.
26 el pueblo de Belén y Netofa, 188;
Mutanen Betlehem da na Netofa 188
27 el pueblo de Anatot, 128;
na Anatot 128
28 el pueblo de Bet-azmavet 42;
na Bet-Azmawet 42
29 el pueblo de Quiriat-jearim, Cafira y Beerot, 743;
na Kiriyat Yeyarim, Kefira da na Beyerot 743
30 el pueblo de Ramá y Geba, 621;
na Rama da na Geba 621
31 el pueblo de Micmas, 122;
na Mikmash 122
32 el pueblo de Bet-el y Ai, 123;
na Betel da na Ai 123
33 el pueblo del otro Nebo, 52;
na ɗayan Nebo 52
34 los hijos del otro Elam, 1.254;
na ɗayan Elam 1,254
35 los hijos de Harim, 320;
na Harim 2 320
36 los hijos de Jericó, 345;
na Yeriko 345
37 los hijos de Lod, Hadid y Ono, 721;
na Lod, da na Hadid, da na Ono 721
38 los hijos de Senaa, 3.930.
na Sena’a 3,930.
39 Este es el número de los sacerdotes: los hijos de Jedaías (por la familia de Jesúa), 973;
Ga zuriyar Firistoci. Zuriyar Yedahiya (ta wurin iyalin Yeshuwa) 973
40 los hijos de Imer, 1.052;
ta Immer 1,052
41 los hijos de Pasur, 1.247;
ta Fashhur 1,247
42 los hijos de Harim, 1.017.
ta Harim 1,017.
43 Este es el número de los levitas: los hijos de Jesúa por Cadmiel (hijos de Hodavías), 74;
Ga zuriyar Lawiyawa. Zuriyar Yeshuwa da Kadmiyel (ta wurin Hodeba) 74.
44 los cantores de los hijos de Asaf, 148;
Mawaƙa. Zuriyar Asaf mutum 148.
45 los porteros de las familias de Salum, Ater, Talmón, Acub, Hatita y Sobai, 138.
Ga zuriyar Matsaran Ƙofofi. Zuriyar Shallum, Ater, Talmon, Akkub, Hatita da Shobai 138.
46 Los descendientes de estos servidores del Templo: Ziha, Hasufa, Tabaot,
Ma’aikatan haikali. Zuriyar Ziha, Hasufa, Tabbawot,
47 Queros, Sia, Padón,
da ta Keros, da ta Siya, da ta Fadon,
48 Lebana, Hagaba, Salmai,
da ta Lebana, da ta Hagaba, da ta Shalmai,
49 Hanán, Gidel, Gahar,
da ta Hanan, da ta Giddel, da ta Gahar,
50 Reaía, Rezín, Necoda,
da ta Reyahiya, da ta Rezin, da ta Nekoda,
51 Gazam, Uza, Paseah,
da ta Gazzam, da ta Uzza, da ta Faseya,
52 Besai, Mehunim, Nefusim,
da ta Besai, da ta Meyunawa, da ta Nefussiyawa,
53 Bacbuc, Hacufa, Harhur,
da ta Bakbuk, da ta Hakufa, da ta Harhur,
54 Bazlut, Mehída, Harsa,
da ta Bazlit, da ta Mehida, da ta Harsha,
55 Barcos, Sísara, Tema,
da ta Barkos, da ta Sisera, da ta Tema,
56 Nezía, y Hatifa.
da ta Neziya, da kuma ta Hatifa.
57 Los descendientes de los siervos del rey Salomón: Sotai, Soferet, Perida,
Ga zuriyar bayin Solomon. Zuriyar Sotai, da ta Soferet, da ta Ferida,
58 Jaala, Darcón, Gidel,
da ta Ya’ala, da ta Darkon, da ta Giddel,
59 Sefatías, Hatil, Poqueret-hazebaim y Amón.
Shefatiya, Hattil, Fokeret-Hazzebayim, da Amon.
60 El total de los siervos del Templo y de los descendientes de los siervos de Salomón era de 392.
Zuriyar ma’aikatan haikali da ta bayin Solomon su 392.
61 Los que procedían de las ciudades de Tel-mela, Tel-Harsa, Querub, Addán e Imer no podían demostrar su genealogía familiar, ni siquiera que eran descendientes de Israel.
Waɗansu sun hauro daga garuruwan Tel-Mela, Tel-Harsha, Kerub, Addon da Immer, amma ba su iya nuna cewa iyalansu su zuriyar Isra’ila ce ba,
62 Entre ellos estaban las familias de Delaía, Tobías y Necoda, 642 en total.
zuriyar Delahiya, Tobiya, da Nekoda 642.
63 Además había tres familias sacerdotales, hijos de Habaía, Cos y Barzilai. (Barzilai se había casado con una mujer descendiente de Barzilai de Galaad, y se llamaba por ese nombre).
Na wajen firistoci kuwa su ne, Zuriyar Hobahiya, da ta Hakkoz, da ta Barzillai (wani mutumin da ya auri’yar Barzillai mutumin Gileyad, aka kuma kira shi da wannan suna).
64 Se buscó un registro de ellos en las genealogías, pero no se encontraron sus nombres, por lo que se les prohibió servir como sacerdotes.
Waɗannan ne aka nemi sunayensu a cikin tarihin asalin iyalai, amma ba a same su a ciki ba, saboda haka aka hana su shiga cikin firistoci, sun zama kamar marasa tsarki.
65 El gobernador les ordenó que no comieran nada de los sacrificios del santuario hasta que un sacerdote pudiera preguntar al Señor sobre el asunto utilizando el Urim y el Tumim.
Sai gwamna ya umarce su kada su ci wani abinci mafi tsarki, sai akwai firist da zai nemi nufin Ubangiji ta wurin Urim da Tummim.
66 El total de personas que regresaron fue de 42.360.
Yawan jama’ar duka ya kai mutum 42,360,
67 Además había 7.337 sirvientes y 245 cantores y cantoras.
ban da bayinsu maza da mata 7,337. Suna kuma da mawaƙa maza da mata 245.
68 Tenían 736 caballos, 245 mulas,
Akwai dawakai 736, alfadarai 245
69 435 camellos y 6.720 burros.
raƙuma 435, da kuma jakuna 6,720.
70 Algunos de los jefes de familia hicieron contribuciones voluntarias para el trabajo. El gobernador entregó a la tesorería 1.000 dáricos de oro, 50 cuencos y 530 conjuntos de ropa para los sacerdotes.
Waɗansu shugabannin iyalai suka ba da kyautai domin taimakon aiki. Gwamna ya ba da darik 1,000 na zinariya, kwanoni 50, da riguna 530 don firistoci.
71 Algunos de los jefes de familia donaron al tesoro para la obra 20.000 dáricos de oro y 2.200 minas de plata.
Waɗansu shugabannin iyalai sun ba da darik 20,000 na zinariya da mina 2,200 na azurfa don aiki.
72 El resto del pueblo donó 20.000 dáricos de oro, 2.000 minas de plata y 67 conjuntos de ropa para los sacerdotes.
Jimillar da sauran mutane suka bayar ta kai darik 20,000 na zinariya, minas 2,000 na azurfa, da riguna sittin da bakwai don firistoci.
73 Los sacerdotes, los levitas, los porteros, los cantores y los servidores del Templo, así como parte del pueblo y el resto de los israelitas, volvieron a vivir en sus pueblos específicos. En el séptimo mes los israelitas vivían en sus pueblos,
Firistoci, da Lawiyawa, da matsaran ƙofofi, da mawaƙa, da ma’aikatan haikali tare da waɗansu mutane da kuma sauran mutanen Isra’ila, suka zauna a garuruwansu. Da wata na bakwai ya zo, Isra’ilawa kuwa sun riga sun zauna a garuruwansu,

< Nehemías 7 >