< Levítico 18 >

1 El Señor le dijo a Moisés:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 “Dile a los israelitas: Yo soy el Señor tu Dios.
“Yi wa Isra’ilawa magana ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ni ne Ubangiji Allahnku.
3 No sigas los caminos de Egipto, donde vivías, y no sigas los caminos de Canaán, donde te llevaré. No adoptes sus prácticas.
Kada ku yi yadda suke yi a Masar inda da kuke zama, kuma ba a ku yi kamar yadda suke yi a ƙasar Kan’ana inda nake kawo ku ba. Kada ku yi yadda suke yin abubuwa.
4 Haz lo que te digo y guarda mis reglas. Yo soy el Señor tu Dios.
Dole ku kiyaye dokokina kuma ku lura ku bi farillaina. Ni ne Ubangiji Allahnku.
5 Si guardas mis reglas y haces lo que te digo, vivirás. Yo soy el Señor.
Ku kiyaye farillaina da dokokina, gama mutumin da ya aikata waɗannan abubuwa zai rayu ta wurinsu. Ni ne Ubangiji.
6 “No tengas relaciones sexuales con un pariente cercano.
“‘Kada wani ya kusaci wani dangi na kusa don yă yi jima’i. Ni ne Ubangiji.
7 No avergüences a tu padre teniendo sexo con tu madre. Ella es tu madre; no tengas sexo con ella.
“‘Kada ka ƙasƙantar da mahaifinka ta wurin kwana da mahaifiyarka. Ita mahaifiyarka ce; kada ka yi jima’i da ita.
8 No tengas sexo con ninguna de las esposas de tu padre y avergüenza a tu padre.
“‘Kada ka yi jima’i da matar mahaifinka, wannan zai ƙasƙantar da mahaifinka.
9 No tengas sexo con tu hermana, si es hija de tu padre o de tu madre, o si nació en la misma casa que tú o en otro lugar.
“‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwarka, ko’yar mahaifinka ko’yar mahaifiyarka, ko an haife ta a gida ɗaya da kai ko kuwa a wani wuri dabam.
10 No tengas sexo con tu nieta, la hija de tu hijo o la hija de tu hija, porque eso sería algo vergonzoso para ti.
“‘Kada ka yi jima’i da’yar ɗanka ko’yar’yarka, wannan zai ƙasƙantar da kai.
11 No tengas sexo con la hija de ninguna de las esposas de tu padre y tu padre, ella es tu hermana.
“‘Kada ka yi jima’i da’yar matar mahaifinka wadda aka haifa wa mahaifinka; ita’yar’uwarka ce.
12 No tengas sexo con la hermana de tu padre. Ella es un pariente cercano de tu padre.
“‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwar mahaifinka, ita dangin mahaifinka ne na kusa.
13 No tengas relaciones sexuales con la hermana de tu madre. Ella es un pariente cercano de tu madre.
“‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwar mahaifiyarka, domin ita dangin mahaifiyarka ce na kusa.
14 No avergüences a tu tío teniendo sexo con su esposa. Ella es tu tía.
“‘Kada ka ƙasƙantar da ɗan’uwan mahaifinka ta wurin kusaci matarsa don ka yi jima’i da ita, ita bābarka ce.
15 No tengas sexo con tu nuera. Ella es la esposa de tu hijo. No tengas sexo con ella.
“‘Kada ka yi jima’i da matar ɗanka. Ita matar ɗanka ne; kada ka yi jima’i da ita.
16 No te acuestes con la esposa de tu hermano y avergüénzate de él.
“‘Kada ka yi jima’i da matar ɗan’uwanka; wannan zai ƙasƙanta ɗan’uwanka.
17 No tengas sexo con una mujer y su hija. No tengas sexo con la hija de su hijo o la hija de su hija. Son sus parientes cercanos. Eso es algo que detesto.
“‘Kada ka yi jima’i da mace da kuma’yarta. Kada ka yi jima’i da’yar ɗanta ko’yar’yarta; su danginta ne na kusa. Wannan mugun abu ne.
18 No te cases con la hermana de tu esposa y tengas sexo con ella mientras tu esposa esté viva. Serán esposas hostiles entre sí.
“‘Kada ka auri’yar’uwar matarka ta zama kishiyar matarka ka kuma yi jima’i da ita yayinda matarka tana da rai.
19 No tengas sexo con una mujer durante el tiempo que esté sucia debido a su período.
“‘Kada ka kusaci mace don ka yi jima’i da ita a lokacin ƙazantar al’adarta.
20 No cometas ningún acto sexual con la esposa de otro hombre. Esto te contaminaría y te haría sucio.
“‘Kada ka yi jima’i da matar maƙwabcinka ka ƙazantar da kanka tare da ita.
21 “No le des ninguno de tus hijos como sacrificio humano a Moloc, porque no debes deshonrar el carácter de tu Dios. Yo soy el Señor.
“‘Kada ku ba da wani daga cikin’ya’yanku don a yi hadaya wa Molek, gama ba za ku ƙasƙantar da sunan Allahnku ba. Ni ne Ubangiji.
22 “No tengas sexo con un hombre como con una mujer. Eso es algo asqueroso.
“‘Kada ka kwana da namiji kamar yadda namiji yakan kwana da ta mace, wannan abin ƙyama ne.
23 No tengas sexo con ningún animal. Esto te contaminaría y te ensuciaría.
“‘Kada ka yi jima’i da dabba ka ƙazantar da kanka. Mace ba za tă ba da kanta ga dabba don yă yi jima’i da ita ba; wannan abin ƙyama ne.
24 Una mujer no debe entregarse a un animal para tener sexo con él. Eso es algo asqueroso. No se contaminen y se ensucien haciendo algo así. Esa es la razón por la que estoy expulsando a estas naciones de la tierra, se han contaminado a sí mismos por todas estas prácticas.
“‘Kada ku ƙazantar da kanku da wani daga cikin waɗannan, domin haka al’umman da zan kora a gabanku suka ƙazantu.
25 Incluso la tierra se ha contaminado, así que la estoy castigando por los pecados cometidos por la gente que vive allí, y la tierra los vomitará.
Har ƙasar ma ta ƙazantu, saboda haka na hukunta ta saboda zunubinta, ƙasar kuwa ta amayar da mazaunanta.
26 “Peroustedes deben hacer lo que yo os diga y guardar mis reglas. No deben hacer ninguno de estos actos repugnantes, ya sea un israelita o un extranjero que viva entre ustedes.
Amma dole ku kiyaye farillaina da kuma dokokina. Kada haifaffe ɗan ƙasa da baƙin da suke zama a cikinku yă yi wani daga cikin waɗannan abubuwa banƙyama,
27 Las personas que vivían en la tierra antes de ti practicaban todas estas cosas repugnantes, y la tierra se contaminó.
gama mutanen da suka zauna a wannan ƙasa kafin ku sun aikata dukan waɗannan abubuwa, suka kuma ƙazantu.
28 Si contaminas la tierra, te vomitará como lo hizo con las naciones anteriores a ti.
Kuma in kuka ƙazantar da ƙasar, za tă amayar da ku kamar yadda ta amayar da al’umman da suka riga ku.
29 “Por consiguiente, cualquiera que haga cualquiera de estas cosas repugnantes debe ser expulsado de su pueblo.
“‘Duk wanda ya yi wani daga cikin waɗannan abubuwa banƙyama, dole a fid da mutumin daga cikin mutanensa.
30 Debes aceptar mi demanda de que no sigas ninguna de estas prácticas repugnantes hechas antes de tu llegada. No se contaminen ni se hagan impuros. Yo soy el Señor su Dios”.
Ku kiyaye umarnaina kuma kada yi ku wata al’ada mai banƙyamar da aka yi kafin ku zo kuma kada ku ƙazantar da kanku da su. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”

< Levítico 18 >