< Lamentaciones 3 >

1 Soy el hombre que ha experimentado el sufrimiento bajo la vara de la ira de Dios.
Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
2 Me ha alejado, obligándome a caminar en las tinieblas en lugar de la luz.
Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
3 De hechome golpea una y otra vez todo el día.
ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
4 Me ha desgastado; me ha hecho pedazos.
Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
5 Me ha asediado, rodeándome de amargura y miseria.
Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
6 Me ha obligado a vivir en las tinieblas, como los muertos desde hace tiempo.
Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
7 Ha levantado un muro a mi alrededor para que no pueda escapar; me ha atado con pesadas cadenas.
Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
8 Aunque siga clamando por ayuda, se niega a escuchar mi oración.
Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
9 Ha puesto piedras en mi camino y me envía por senderos torcidos.
Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
10 Es un oso que me acecha, un león escondido listo para atacar,
Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
11 Me arrastró de mi camino y me hizo pedazos, dejándome indefenso.
ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
12 Cargó su arco con una flecha y me usó como blanco,
Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
13 Me disparó en los riñones con sus flechas.
Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
14 Ahora todos se ríen de mí, cantando canciones que se burlan de mí todo el día.
Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
15 Me ha llenado de amargura; me ha llenado de amargo ajenjo.
Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
16 Me ha roto los dientes con arenilla; me ha pisoteado en el polvo.
Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
17 Me ha arrancado la paz; he olvidado todo lo bueno de la vida.
An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
18 Por eso digo: Mi expectativa de una larga vida ha desaparecido, junto con todo lo que esperaba del Señor.
Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
19 No olvides todo lo que he sufrido en mi agonía, tan amargo como el ajenjo y el veneno.
Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
20 Ciertamente no lo he olvidado. Lo recuerdo demasiado bien, por eso me hundo en la depresión.
Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
21 Pero aún tengo esperanza cuando pienso en esto:
Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
22 Es por el amor fiel del Señor que nuestras vidas no están destruidas, pues con sus actos de misericordia nunca nos abandona.
Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
23 Él los renueva cada mañana. ¡Qué maravillosamente fiel eres, Señor!
Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
24 El Señor es todo lo que necesito, me digo a mí mismo: Pondré mi esperanza en él.
Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
25 El Señor es bueno con los que confían en él, con cualquiera que lo siga.
Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
26 Es bueno esperar tranquilamente la salvación del Señor.
yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
27 Es bueno que el ser humano aprenda a soportar con paciencia la disciplina mientras es joven.
Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
28 Debe sentarse solos en silencio, porque es Dios quien lo ha disciplinado.
Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
29 Debe inclinarse con el rostro hacia el suelo, porque aún puede haber esperanza.
Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
30 Debe poner la mejilla a quien quiera abofetearlos; debe aceptar los insultos de los demás.
Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
31 Porque el Señor no nos abandonará para siempre.
Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
32 Aunque nos venga la tristeza, él nos muestra misericordia porque su amor fiel es muy grande.
Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
33 Porque no quiere herir ni causarle dolor a ninguno.
Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
34 Ya sea que alguien maltrate a todos los prisioneros de la tierra
Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
35 Ole niegue a alguien sus derechos mientras el Altísimo lo ve,
ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
36 O sea que alguien engañe a otro en su caso legal, estas son cosas el Señor noaprueba.
ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
37 ¿Quién habló y llegó a existir? ¿No fue el Señor quien lo ordenó?
Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
38 Cuando el Altísimo habla puede ser para un desastre o para una bendición.
Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
39 ¿Por qué habría de quejarse un ser humano de las consecuencias de sus pecados?
Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
40 Debemos mirarnos a nosotros mismos, examinar nuestros actos y volver al Señor.
Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
41 No nos limitemos a levantar la mano a Dios hacia el cielo, sino nuestra mente también, y digamos:
Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
42 “Nosotros somos pecadores; nosotros somos rebeldes ¡y tú no nos has perdonado!”
“Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
43 Te has envuelto en ira y nos has perseguido, matándonos sin piedad. Has destruido sin piedad.
“Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
44 Te has envuelto en una nube que ninguna oración puede penetrar.
Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
45 Nos has convertido en residuos y desechos para las naciones de alrededor.
Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
46 Todos nuestros enemigos abren la boca para criticarnos.
“Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
47 Estamos aterrorizados y atrapados, devastados y destruidos.
Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
48 Las lágrimas brotan de mis ojos por la muerte de mi pueblo.
Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
49 Mis ojos rebosan de lágrimas todo el tiempo. No se detendrán
Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
50 Hasta que el Señor mire desde el cielo y vea lo que pasa.
Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
51 Lo que he visto me atormenta por lo que ha sucedido a todas las mujeres de mi ciudad.
Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
52 Sin razón alguna mis enemigos me atraparon como a un pájaro.
Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
53 Intentaron matarme arrojándome a un pozo y tirándome piedras.
Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
54 El agua me inundó hastala cabeza, y pensé que moriría.
ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
55 Desde lo más profundo de la fosa te llamé, Señor.
Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
56 Tú me oíste cuando oré: “Por favor, no ignores mi grito de auxilio”.
Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
57 Viniste a mí cuando te llamé, y me dijiste: “¡No tengas miedo!”
Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
58 ¡Has tomado mi caso y me has defendido; has salvado mi vida!
Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
59 Señor, tú has visto las injusticias que se han cometido contra mí; ¡Defiéndeme, por favor!
Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
60 Has observado lo vengativos que son y las veces que han conspirado contra mí.
Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
61 Señor, tú has oído cómo me han insultado y lo que han tramado contra mí,
Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
62 ¡Cómo mis enemigos hablan contra mí y se quejan de mí todo el tiempo!
Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
63 ¡Mira! Ya sea que estén sentados o de pie, siguen burlándose de mí en sus canciones.
Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
64 ¡Págales como se merecen, Señor, por todo lo que han hecho!
Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
65 Dales algo para que sus mentes queden cubiertas! ¡Que tu maldición caiga sobre ellos!
Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
66 Persíguelos en tu cólera, Señor, y deshazte de ellos de la tierra!
Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.

< Lamentaciones 3 >