< Job 36 >

1 Elihú continuó hablando.
Elihu ya ci gaba,
2 “Ténganme un poco más de paciencia y déjenme explicarles. Todavía tengo algo que decir en nombre de Dios.
“Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
3 Compartiré mis amplios conocimientos, y demostraré que mi Creador tiene razón.
Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
4 Les aseguro que lo que digo no son mentiras, pues soy un hombre cuyos conocimientos son de primer orden.
Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
5 Dios es poderoso, pero no desprecia a nadie; es poderoso en fuerza y comprensión.
“Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
6 No mantiene vivo al impío, sino que hace justicia al oprimido.
Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
7 Siempre presta atención a los que hacen el bien, y los coloca en tronos con los reyes, honrándolos eternamente.
Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
8 Si están encadenados, atados con cuerdas de sufrimiento,
Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
9 entonces les explica lo que han hecho: sus pecados arrogantes.
yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
10 Les hace prestar atención y les ordena que dejen de pecar.
Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
11 “Si escuchan y hacen lo que Dios dice, vivirán su vida con felicidad.
In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
12 Pero si no escuchan, tendrán una muerte violenta, ignorantes de Dios.
Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
13 Los que rechazan a Dios se aferran a su amargura. Incluso cuando él los disciplina, no claman a él por ayuda.
“Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
14 Mueren en su juventud; su vida termina entre los hombres que se prostituyen en el templo.
Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
15 A través del sufrimiento, Dios salva a los que sufren; consigue su atención a través de sus problemas.
Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
16 “Dios está tratando de rescatarte de las fauces de los problemas a un lugar de libertad y seguridad, llenando tu mesa con los mejores alimentos.
“Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
17 Pero tú te preocupas por la suerte de los malvados; el juicio y la justicia llenan tu mente.
Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
18 Pero ten cuidado de que tu cólera no te seduzca en la burla; y no dejes que el tamaño del ‘soborno’ te conduzcan al pecado.
Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
19 ¿Tu grito de auxilio te sostendrá cuando vengan los problemas?
Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
20 No anheles la noche en la que las personas son arrebatadas repentinamente.
Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
21 ¡Cuida que no te vuelvas al mal! Porque es por esto que estás siendo probado a través del sufrimiento.
Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
22 “¡Mira qué poder tiene Dios! ¿Qué maestro es como él?
“An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
23 ¿Quién le ha enseñado lo que debe hacer? ¿Quién puede decirle: ‘Has hecho mal’?
Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
24 Al contrario, alábenle por lo que ha hecho, como dicen los cantos.
Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
25 Todo el mundo ha visto la creación de Dios, aunque sólo desde la distancia.
Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
26 “Mira qué grande es Dios, más de lo que podemos entender. Nadie puede contar sus años.
Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
27 Él extrae el agua y la destila en rocío y lluvia.
“Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
28 Las nubes derraman lluvia, cayendo abundantemente sobre la humanidad.
Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
29 ¿Alguien puede entender cómo se extienden las nubes, o cómo ruge el trueno desde donde vive?
Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
30 Mira cómo esparce los rayos a su alrededor, y cubre de oscuridad las profundidades del mar.
Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
31 Con estas acciones gobierna a los pueblos, les proporciona abundante alimento.
Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
32 Tiene el rayo en sus manos y ordena dónde debe caer.
Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
33 El trueno anuncia su presencia: hasta el ganado sabe cuándo se avecina una tormenta”.
Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.

< Job 36 >