< Job 31 >

1 “Me prometí a mí mismo no mirar nunca con deseo a las jóvenes.
“Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
2 ¿Qué debe esperar la gente de Dios? ¿Qué recompensa debe darles el Todopoderoso en lo alto?
Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
3 ¿No es el desastre para los malvados y la destrucción para los que hacen el mal?
Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
4 ¿No ve Dios todo lo que hago, incluso cuenta cada paso que doy?
Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
5 ¿He vivido una vida engañosa? ¿He estado ansioso por decir mentiras?
“In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
6 ¡No! Que Dios me pese en la balanza de su justicia y que descubra mi integridad.
Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
7 “Si me he desviado del camino de Dios, si he dejado que lo que veo se convierta en mis deseos, si hay alguna mancha de pecado en mis manos,
In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
8 entonces que otro coma lo que he sembrado, y que todo lo que he cultivado sea desarraigado.
bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
9 Si una mujer me ha seducido, o si he buscado la oportunidad de acostarme con la mujer de mi prójimo,
“In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
10 que mi esposa sirva a otro, que otros hombres se acuesten con ella.
sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
11 Porque eso sería una maldad, un pecado que merece castigo,
Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
12 porque este pecado es como un fuego que lleva a la destrucción, destruyendo todo lo que tengo.
Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
13 “Si me negara a escuchar a mis siervos o siervas cuando me trajeran sus quejas,
“In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
14 ¿qué haría cuando Dios viniera a juzgarme? ¿Cómo respondería si me investigara?
me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
15 ¿Acaso el mismo Dios no nos hizo a todos?
Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
16 ¿Me he negado a dar a los pobres lo que necesitaban, o he hecho desesperar a las viudas?
“In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
17 ¿Acaso he comido yo solo un trozo de pan? ¿No he compartido siempre mi comida con los huérfanos?
in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
18 Desde que era joven fui padre de los huérfanos y cuidé de las viudas.
amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
19 Si alguna vez veía a alguien necesitado de ropa, a los pobres sin nada que ponerse,
In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
20 siempre me agradecían la ropa de lana que los mantenía calientes.
kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
21 “Si levantaba la mano para golpear a un huérfano, seguro de que si llegaba a los tribunales los jueces estarían de mi parte,
in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
22 entonces que mi hombro sea arrancado de su articulación, que mi brazo sea arrancado de su cavidad.
bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
23 Como me aterra el castigo que Dios me tiene reservado, y debido a su majestad, nunca podría hacer esto.
Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
24 “¿He puesto mi confianza en el oro, llamando al oro fino ‘mi seguridad’?
“In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
25 ¿Me he deleitado en ser rico, feliz por todas mis riquezas que había ganado?
in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
26 ¿He mirado el sol brillando tan intensamente o la luna moviéndose con majestuosidad por el cielo
In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
27 y he tenido la tentación de adorarlos secretamente besando mi mano ante ellos como señal de devoción?
zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
28 Esto también sería un pecado que merece castigo porque significaría que he negado a Dios en lo alto.
Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
29 “¿Alguna vez me he alegrado cuando el desastre destruyó a los que me odiaban, o he celebrado cuando el mal los derribó?
“In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
30 Nunca he permitido que mi boca pecara echando una maldición sobre la vida de alguien.
ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
31 ¿No ha preguntado mi familia: ‘¿Hay alguien que no haya comido todo lo que quería de su comida?’
in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
32 Nunca he dejado dormir a extraños en la calle; he abierto mis puertas a los viajeros.
Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
33 ¿He ocultado mis pecados a los demás, escondiendo mi maldad en lo más profundo de mí?
in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
34 ¿Tenía miedo de lo que pensaran los demás, del desprecio que me hicieran las familias, y por eso me callaba y no salía?
domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
35 “¿Por qué nadie escucha lo que digo? Firmo con mi nombre para avalar todo lo que he dicho. Que el Todopoderoso me responda. Que mi acusador escriba de qué me acusa.
(“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
36 Yo los pondría en alto; Los llevaría en mi cabeza como una corona.
Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
37 Le explicaría todo lo que había hecho; mantendría la cabeza alta ante él.
Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
38 “Si mi tierra ha gritado contra mí; si sus surcos han llorado por mí;
“In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
39 si he tomado sus cosechas sin pago o si he causado daño a los agricultores;
in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
40 entonces que crezcan espinas en lugar de trigo, y cizaña en lugar de cebada”. Las palabras de Job se terminan.
bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.

< Job 31 >