< Job 3 >

1 Después de esto Job comenzó a hablar, maldiciendo el día de su nacimiento.
Bayan wannan Ayuba ya buɗe baki ya la’anta ranar da aka haife shi.
2 Y dijo:
Ayuba ya ce,
3 “Que el día en que nací sea borrado, así como la noche en que se anunció que un niño había sido concebido.
“A hallaka ranar da aka haife ni, da kuma daren da aka ce, ‘An haifi jariri namiji!’
4 Que ese día se convierta en tinieblas. Que el Dios de arriba no lo recuerde. Que no brille la luz sobre él.
Bari ranan nan ta zama duhu; kada Allah yă kula da ita; kada rana tă yi haske a wannan rana.
5 Cúbranlo con oscuridad y sombra de muerte. Una nube negra debería ensombrecerlo. Debería ser tan aterrador como la oscuridad de un eclipse de día.
Bari duhu da inuwa mai duhu ta sāke rufe ta; gizagizai kuma su rufe ta; duhu kuma ya rufe haskenta.
6 Borren esa noche como si nunca hubiera existido. No la cuenten en el calendario. Que no tenga día en ningún mes.
Bari duhu mai yawa yă rufe daren nan; kada a haɗa ta cikin kwanakin shekara, ko kuma cikin kwanakin watanni.
7 “Que en esa noche no nazcan niños, que no se escuchen sonidos de felicidad.
Bari daren yă zama marar amfani; kada a ji wata sowa ta farin ciki.
8 Que la maldigan los que maldicen ciertos días, los que tienen el poder de sacar al Leviatán.
Bari waɗanda suke la’anta ranaku su la’anta wannan rana su waɗanda suke umartar dodon ruwa.
9 Que sus estrellas de la madrugada permanezcan oscuras. Que al buscar la luz, no vea ninguna, que no vea el resplandor del amanecer
Bari taurarinta na safe su zama duhu; bari ranar tă yi ta jiran ganin haske amma kada tă gani,
10 porque no cerró el vientre de mi madre para impedirme ver los problemas.
gama ba tă hana uwata ɗaukar cikina, don ta hana ni shan wahalan nan ba.
11 “¿Por qué no nací muerto? ¿Por qué no morí al nacer?
“Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
12 ¿Por qué hubo un regazo para que me acostara, y pechos para que me amamantaran?
Me ya sa aka haife ni, aka tanada nono na sha na rayu?
13 Ahora estaría acostado en paz, durmiendo y descansando
Da yanzu ina kwance cikin salama; da ina barcina cikin salama
14 junto con los reyes de este mundo y sus funcionarios cuyos palacios ahora yacen en ruinas;
tare da sarakuna da mashawarta a cikin ƙasa, waɗanda suka gina wa kansu wuraren da yanzu duk sun rushe,
15 o con los nobles que coleccionaban oro y llenaban sus casas de plata.
da shugabanni waɗanda suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.
16 ¿Por qué no fui un aborto, enterrado en secreto, un bebé que nunca vio la luz?
Ko kuma don me ba a ɓoye ni a cikin ƙasa kamar jaririn da aka haifa ba rai ba, kamar jaririn da bai taɓa ganin hasken rana ba.
17 Allí, en la tumba, los malvados no dan más problemas, y los que ya no tienen fuerzas tienen su descanso.
A wurin mugaye za su daina yin mugunta, gajiyayyu kuma za su huta.
18 Allí los prisioneros descansan y no escuchan las órdenes de sus opresores.
Waɗanda aka daure za su sami jin daɗin; an sake su ba za su sāke jin ana tsawata masu ba.
19 Tanto los pequeños como los grandes están allí, y los esclavos son liberados de sus amos.
Manyan da ƙanana suna a can, bawa kuma ya sami’yanci daga wurin maigidansa.
20 ¿Por qué Dios da vida a los que sufren, a los que viven amargamente,
“Don me ake ba da haske ga waɗanda suke cikin ƙunci, rai kuma ga masu ɗacin rai
21 a los que esperan una muerte que no llega y a los que buscan la muerte más desesperadamente que la caza de un tesoro?
ga waɗanda suke neman mutuwa amma ba su samu ba, waɗanda suke nemanta kamar wani abu mai daraja a ɓoye,
22 ¡Son tan increíblemente felices cuando llegan a la tumba!
waɗanda suke farin ciki sa’ad da suka kai kabari?
23 ¿Por qué se da luz a quien no sabe a dónde va, a quien Dios ha cercado?
Don me aka ba mutum rai, mutumin da bai san wani abu game da kansa ba, mutumin da Allah ya kange shi.
24 “Mis gemidos son el pan que como, y mis lágrimas son el agua que bebo.
Baƙin ciki ya ishe ni maimakon abinci; ina ta yin nishi ba fasawa;
25 Porque todo lo que temía me ha sucedido; todo lo que temía me ha sobrevenido.
Abin da nake tsoro ya faru da ni; abin da ba na so ya same ni.
26 No tengo paz, ni tranquilidad, ni descanso. Lo único que siento es rabia”.
Ba ni da salama, ba natsuwa; ba ni da hutu, sai wahala kawai.”

< Job 3 >