< Job 29 >

1 Job siguió hablando.
Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
2 “¡Ojalá volviera a los viejos tiempos en que Dios me cuidaba!
“Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
3 Su luz brillaba sobre mí y alumbraba mi camino en la oscuridad.
lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
4 Cuando era joven y fuerte, Dios era mi amigo y me hablaba en mi casa.
Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
5 El Todopoderoso seguía conmigo y estaba rodeado de mis hijos.
lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma’ya’yana suna kewaye da ni,
6 Mis rebaños producían mucha leche, y el aceite fluía libremente de mis prensas de aceitunas.
lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
7 Salí a la puerta de la ciudad y me senté en la plaza pública.
“Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
8 Los jóvenes me veían y se apartaban del camino; los ancianos me defendían.
matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
9 Los dirigentes guardaron silencio y se taparon la boca con las manos.
sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
10 Las voces de los funcionarios se acallaron; se callaron en mi presencia.
Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
11 “Todos los que me escuchaban me alababan; los que me veían me elogiaban,
Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
12 porque daba a los pobres que me llamaban y a los huérfanos que no tenían quien los ayudara.
domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
13 Los que estaban a punto de morir me bendijeron; hice cantar de alegría a la viuda.
Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
14 Siendo sincero y actuando correctamente eran lo que yo llevaba como ropa.
Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
15 Fui como los ojos para los ciegos y los pies para los cojos.
Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
16 Fui como un padre para los pobres, y defendí los derechos de los extranjeros.
Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
17 Rompí la mandíbula de los malvados y les hice soltar su presa de los dientes.
Na karya ƙarfin mugaye na ƙwato waɗanda suke riƙe da haƙoransu.
18 Pensé que moriría en casa, después de muchos años.
“Na yi tunani cewa, ‘Zan mutu a cikin gidana, kwanakina da yawa kamar turɓayar ƙasa.
19 Como un árbol, mis raíces se extienden hasta el agua; el rocío se posa en mis ramas durante la noche.
Jijiyoyina za su kai cikin ruwa, kuma raɓa za tă kwanta a rassana dukan dare.
20 Siempre se me concedían nuevos honores; mi fuerza se renovaba como un arco infalible.
Ɗaukakata za tă kasance tare da ni garau, bakana koyaushe sabo ne a hannuna.’
21 “La gente escuchaba atentamente lo que yo decía; se callaba al escuchar mis consejos.
“Mutane suna mai da hankali su saurare ni, suna yin shiru don su ji shawarata.
22 Una vez que yo hablaba, no tenían nada más que decir; lo que yo decía era suficiente.
Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba. Maganata ta shige su.
23 Me esperaban como quien espera la lluvia, con la boca abierta por la lluvia de primavera.
Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama. Sukan sha daga cikin maganganuna kamar mai shan ruwan bazara.
24 Cuando les sonreía, apenas podían creerlo; mi aprobación significaba todo el mundo para ellos.
Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda; hasken fuskata yana da daraja a gare su.
25 Decidí el camino a seguir como su líder, viviendo como un rey entre sus soldados, y cuando estaban tristes los consolaba”.
Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin rundunansu; ina nan kamar mai yi wa masu makoki ta’aziyya.

< Job 29 >