< Job 27 >

1 Job comenzó a hablar de nuevo.
Ayuba kuwa ya ci gaba da magana,
2 “Les prometo que, mientras viva Dios, que me ha negado la justicia; el Todopoderoso, que me ha amargado la vida,
“Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.
3 mientras tenga vida, mientras el aliento de Dios permanezca en mis fosas nasales,
Muddin ina da rai a cikina kuma numfashin Allah yana cikin hancina,
4 mis labios nunca dirán mentiras, mi lengua nunca será deshonesta.
bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
5 Nunca aceptaré que tengan la razón; insistiré en mi inocencia hasta el día de mi muerte.
Ba zan taɓa yarda cewa kuna da gaskiya ba; har in mutu, ba zan daina kāre mutuncina ba.
6 Estoy convencido de que tengo razón y nunca dejaré de creerlo; mi conciencia no me condenará mientras viva.
Zan ci gaba da adalcina, ba zan fasa ba; lamirina ba zai taɓa yashe ni ba, dukan kwanakin raina.
7 “Que mi enemigo se vuelva como los malvados; que los que se oponen a mí se vuelvan como los que hacen el mal.
“Bari maƙiyana su zama kamar mugaye, masu gāba da ni kuma su zama kamar marasa adalci.
8 Porque, ¿qué esperanza tienen los que rechazan a Dios, cuando él los derribe, cuando Dios ponga fin a sus vidas?
Gama wane bege marar tsoron Allah yake da shi, lokacin da aka datse shi, lokacin da Allah ya ɗauke ransa?
9 Cuando les lleguen tiempos de angustia, ¿escuchará Dios su grito de auxilio?
Ko Allah yana sauraron kukansa lokacin da ƙunci ya auko masa?
10 ¿Tienen una buena relación con el Todopoderoso? ¿Pueden invocar a Dios en cualquier momento?
Ko zai sami farin ciki daga Maɗaukaki? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
11 Permítanme explicarles el poder de Dios. No voy a retener nada de lo que el Todopoderoso ha planeado.
“Zan koya muku game da ikon Allah; ba zan ɓoye hanyoyin Maɗaukaki ba.
12 Si todos ustedes han reconocido esto, ¿por qué hablan de tonterías tan vanas?
Duk kun ga wannan ku da kanku saboda haka me ya sa kuke maganganun nan marasa ma’ana?
13 “Esto es lo que Dios dispone como destino para los malvados, esta es la herencia que los despiadados recibirán del Todopoderoso,
“Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.
14 aunque tengan muchos hijos, experimentarán muertes violentas o morirán de hambre.
Kome yawan’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.
15 Los que sobrevivan morirán de enfermedad, y ni siquiera sus viudas se lamentarán por ellos.
Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
16 Aunque amontonen plata como polvo y ropa como montones de barro,
Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
17 los que hacen el bien se pondrán la ropa y los inocentes se repartirán la plata.
abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
18 Construyen sus casas como la polilla; como un endeble refugio hecho por un vigilante.
Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
19 Se acuestan ricos, pero nunca más. Porque cuando se despiertan, todo ha desaparecido.
Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.
20 Olas de pánico los inundan; en la noche un torbellino los arrebata.
Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.
21 El viento del este los levanta y se van, llevados lejos de donde estaban.
Iskar gabas za tă tafi da shi; shi ke nan ya ƙare; za tă share shi daga wurinsa.
22 El viento los golpea con toda su fuerza; intentan escapar desesperadamente.
Za tă murɗe shi ba tausayi, lokacin da yake guje wa ikon iskar.
23 Las personas aplaudirles y sisearles allí donde estén”.
Zai tafa hannu yă yi tsaki yă kawar da shi daga wurinsa.”

< Job 27 >