< Job 20 >

1 Entonces Zofar el naamatita respondió y dijo:
Sai Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
2 “¡Me veo obligado a responder porque estoy muy molesto!
“Tunanin da ya dame ni ya sa dole in amsa domin abin ya dame ni sosai.
3 ¡Lo que te oigo decir me ofende, pero sé cómo responderte!
Na ji wani zargin da ka yi mini na reni, kuma yadda na gane, shi ya sa zan ba da amsa.
4 “¿No sabes que desde la antigüedad, desde que los seres humanos fueron puestos en esta tierra,
“Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
5 el triunfo de los malvados no dura mucho tiempo, y que los que rechazan a Dios sólo son felices por poco tiempo?
mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
6 Aunque sean tan altos que lleguen a los cielos, aunque sus cabezas toquen las nubes,
Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
7 se desvanecerán para siempre como sus propios excrementos. Las personas que los conocían
Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
8 se desvanecerán como un sueño, para no ser encontrados nunca, huyendo como una visión de la noche.
Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
9 Los que una vez los vieron no los verán más; sus familias no volverán a poner los ojos en ellos.
Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
10 Sus hijos tendrán que pagar a los pobres y tendrán que devolver sus riquezas.
Dole’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.
11 Aunque los malvados tengan cuerpos jóvenes y fuertes, morirán y serán enterrados.
Jin ƙarfi da ya cika ƙasusuwansa zai kwantar da shi a cikin ƙura.
12 “Aunque el mal sabe dulce en sus bocas y lo esconden bajo sus lenguas,
“Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
13 no lo dejan ir sino que lo mantienen en sus bocas,
ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
14 y en sus estómagos se vuelve amargo, volviéndose como veneno de serpiente dentro de ellos.
duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
15 Se tragan las riquezas y las vuelven a vomitar; Dios las expulsa de sus estómagos.
Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
16 Aspiran veneno de serpiente; la mordedura de la víbora los matará.
Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
17 No vivirán para disfrutar de los arroyos, de los ríos de leche y miel.
Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
18 Tendrán que devolver lo que han ganado y no tendrán ningún beneficio; no disfrutarán de ninguna de sus ganancias.
Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
19 Porque han oprimido y han abandonado a los pobres; se han apoderado de casas que no construyeron.
Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
20 Porque su codicia nunca fue satisfecha, no queda nada que les guste y que no hayan consumido.
“Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
21 Nada escapa a sus voraces apetitos, por lo que su felicidad no dura mucho.
Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
22 “Incluso cuando los malvados tienen todo lo que desean, se enfrentan a problemas; toda clase de miseria caerá sobre ellos.
Yana cikin samun arziki, ɓacin rai zai auka masa; ƙunci mai ƙarfi zai zo masa.
23 Mientras están ocupados llenando sus estómagos, la hostilidad de Dios arderá contra ellos, y caerá como lluvia sobre ellos.
Lokacin da ya cika cikinsa, Allah zai zuba fushinsa a kansa, zai daddaka shi.
24 Mientras huyen para escapar de un arma de hierro, una flecha de bronce los alcanzará.
Ko da yake yana guje wa makamin ƙarfe, kibiya mai bakin tagulla za tă huda shi.
25 La flecha sale de su vesícula biliar, brillando con sangre. Están absolutamente aterrorizados.
Zai zāre ta daga bayansa, tsinin zai fita daga hantarsa; tsoro zai cika shi;
26 Todo lo que valoran desaparecerá en la oscuridad; el fuego divino los destruirá; todo lo que les queda se convertirá en humo.
duhu kawai yake jiran dukiyarsa. Wutar da ba a fifita ba za tă cinye shi ta kuma ƙona duk abin da ya rage a tentinsa.
27 Los cielos revelarán lo que han hecho mal; la tierra se levantará contra ellos.
Sammai za su fallasa laifinsa; duniya za tă yi gāba da shi.
28 Todos sus bienes serán sacados de sus casas; serán arrastrados en el día del juicio de Dios.
Ambaliyar ruwa za tă tafi da gidansa, ruwaye masu gudu a ranar fushin Allah.
29 Esta es la parte que los impíos reciben de Dios, la herencia que Dios dice que deben tener”.
Abin da Allah zai sa yă faru da mugu ke nan, gādon da Allah ya ba shi ke nan.”

< Job 20 >