< Job 16 >

1 Entonces Job respondió:
Sai Ayuba ya amsa,
2 “Ya he oído todo esto antes. ¡Son consoladores que sólo causan problemas!
“Na ji abubuwa da yawa kamar waɗannan; dukanku ba ku iya ta’aziyya ba!
3 ¿No cesarán sus discursos que son como el viento? ¿Qué les molesta tanto como para que tengan que responderme?
Dogayen surutanku ba sa ƙare ne? Me yake sa kuke ta yin waɗannan surutai har kuke cin gaba da yin gardama?
4 Podría hablar como si ustedes estuvieran en mi lugar, encadenando palabras para criticarlos, ridiculizándolos con un movimiento de cabeza.
Ni ma zan iya yin maganganu kamar yadda kuke yi in da kuna cikin halin da nake; zan iya faɗar duk abubuwan da kuke faɗi, in kaɗa muku kaina.
5 Podría edificarlos con mi boca diciendo palabras; el movimiento de mis labios aliviaría su dolor.
Amma bakina zai ƙarfafa ku; ta’aziyyar da za tă fito daga bakina za tă kawar muku da ɓacin zuciyarku.
6 Para mí, si hablo no se alivia mi dolor, y si no hablo el dolor sigue ahí.
“Duk da haka in na yi magana, ba na samun sauƙi; in ma na yi shiru zafin ba ya tafiya.
7 “Dios, me has agotado. Has destruido a toda mi familia.
Ba shakka ya Allah ka gajiyar da ni; ka ɓata gidana gaba ɗaya.
8 Me has hecho marchitar, lo cual es un testimonio contra mí; mi cuerpo delgado atestigua contra mí.
Ka daure ni, ya kuma zama shaida; yadda na rame sai ƙasusuwa, wannan ya sa ake gani kamar don ni mai zunubi ne shi ya sa.
9 Me ha desgarrado en su cólera; en su hostilidad ha rechinado los dientes contra mí; mi enemigo me atraviesa con su mirada feroz.
Allah ya kai mini hari ya yi kaca-kaca da ni cikin fushinsa yana cizon haƙoransa don fushin da yake yi da ni; ya zura mini ido.
10 La gente me mira con la boca abierta, me abofetean en las mejillas para burlarse de mí, se agolpan a mi alrededor para atacarme.
Mutane suka buɗe baki suka yi mini riyar reni; suka yi mini ba’a suka haɗu suka tayar mini.
11 Dios me ha entregado a la gente malvada; me ha arrojado en sus manos.
Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefa ni hannun mugaye.
12 “Yo vivía en paz y él me hizo pedazos. Me agarró por el cuello y me hizo pedazos. Me ha convertido en su blanco.
Dā ina zamana lafiya kome yana tafiya daidai; amma ya ragargaza ni; ya shaƙe ni a wuya; ya murƙushe ni na zama abin barata gare shi;
13 Sus arqueros me rodean. Sus flechas atraviesan mis riñones sin piedad. Derrama mi hiel por el suelo.
maharbansa sun kewaye ni. Ba tausayi, ya soke ni a ƙodata har jini ya zuba a ƙasa.
14 Como un muro me derriba, brecha tras brecha, se abalanza sobre mí como un guerrero.
Ya ji mini rauni a kai a kai ya auko mini kamar mai yaƙi.
15 He sembrado tela de silicio para cubrir mi piel; mi fuerza yace rota en el polvo.
“Ina makoki saye da tsummoki na ɓoye fuskata a cikin ƙura.
16 Mi cara está roja de tanto llorar y sombras oscuras rodean mis ojos,
Fuskata ta yi ja don kuka idanuna sun kukumbura;
17 aunque no he hecho nada malo y mi oración es pura.
duk da haka hannuwana ba su aikata ɓarna ba kuma addu’ata mai tsabta ce.
18 “Tierra, no cubras mi sangre. Que mi grito no encuentre lugar para esconderse.
“Ya duniya, kada ki ɓoye jinina; bari yă yi kuka a madadina!
19 Mira, ahora mismo mi testigo está en el cielo; el que habla por mí está en las alturas.
Ko yanzu haka shaidata tana sama; wanda zai tsaya mini yana sama.
20 Mis amigos me desprecian, pero mis ojos derraman lágrimas ante Dios.
Shi mai yin roƙo a madadina abokina ne yayinda nake kuka ga Allah;
21 Quiero que mi testigo hable por mí ante Dios como quien habla por su amigo.
a madadin mutum ya yi roƙo ga Allah kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.
22 Porque dentro de pocos años andaré por ese camino del que no volveré”.
“Shekaru kaɗan suka rage in kama hanyar da ba a komawa.

< Job 16 >