< Job 11 >

1 Entonces Zofar, el naamatita, comenzó a hablar y dijo:
Sa’an nan Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
2 “¿Acaso no hay que responder a tantas palabras? ¿O se demuestra que una persona tiene razón por hablar mucho?
“Duk surutun nan ba za a amsa maka ba? Ko mai surutun nan marar laifi ne?
3 ¿Debería todo tu parloteo obligar a la gente a callarse? Cuando te burlas, ¿no debería alguien hacerte sentir avergonzado?
Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
4 Tú has dicho: ‘Lo que enseño es la pura verdad’, y ‘a los ojos de Dios estoy limpio’.
Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
5 Si tan solo Dios hablara y te lo dijera directamente,
Da ma Allah zai yi magana, yă buɗe baki yă faɗi wani abin da ka yi da ba daidai ba
6 porque entonces te explicaría los secretos de la sabiduría. La verdadera sabiduría tiene muchas caras. El trato de Dios hacia ti es mucho mejor de lo que merece tu culpa.
yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.
7 “¿Puedes descubrir los misterios de Dios? ¿Puedes descubrir toda la sabiduría del Todopoderoso?
“Ko za ka iya gane al’amuran Allah? Ko za ka iya gane girman asirin Maɗaukaki?
8 Es más grande que los cielos, ¿qué puedes hacer? Es más profundo que el Seol, ¿qué puedes saber? (Sheol h7585)
Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol h7585)
9 Se extiende más allá de la tierra y es más ancho que el mar.
Tsayinsu ya fi tsawon duniya da kuma fāɗin teku.
10 Si Dios viene y encarcela a alguien, o reúne al tribunal para juzgarlo, ¿quién puede detenerlo?
“In ya zo ya kulle ka a kurkuku ya ce kai mai laifi ne, wa zai hana shi?
11 Porque Dios sabe quiénes son los que engañan: cuando ve que alguien peca, él pone su atención en él.
Ba shakka yana iya gane mutanen da suke marasa gaskiya; kuma in ya ga abin da yake mugu, ba ya kula ne?
12 Los tontos se volverán sabios cuando los asnos salvajes nazcan mansos!
Amma daƙiƙin mutum ba ya taɓa zama mai hikima kamar dai a ce ba a taɓa haihuwar ɗan aholaki horarre.
13 “Pero si te arrepientes y extiende tus manos para rezarle,
“Duk da haka in ka miƙa masa zuciyarka, ka kuma miƙa hannuwanka gare shi,
14 si te deshaces de tus pecados y no dejas que la maldad continúe en tu vida,
in ka kawar da zunubin da yake hannunka, ba ka bar zunubi ya kasance tare da kai ba
15 entonces serás capaz de mantener la cabeza alta en la inocencia, estarás firme y sin miedo.
shi ne za ka iya ɗaga fuskarka ba tare da jin kunya ba; za ka tsaya da ƙarfi kuma ba za ka ji tsoro ba.
16 Olvidarás tu miseria, recordándola sólo como agua bajo el puente.
Ba shakka za ka manta da wahalolinka, za ka tuna da su kamar yadda ruwa yake wucewa.
17 Tu vida brillará más que el sol del mediodía; incluso la oscuridad será como la mañana.
Rayuwarka za tă fi hasken rana haske, duhu kuma zai zama kamar safiya.
18 Tendrás confianza porque hay esperanza; estarás protegido y descansarás confiado.
Za ka zauna lafiya, domin akwai bege; za ka duba kewaye da kai ka huta cikin kwanciyar rai.
19 Te acostarás a dormir sin que nadie te asuste, y muchos vendrán a pedir tu favor.
Za ka kwanta, ba wanda zai sa ka ji tsoro, da yawa za su zo neman taimako a wurinka.
20 Pero los ojos de los malvados fallarán, no podrán escapar, y su única esperanza es la muerte”.
Amma idanun mugaye ba za su iya gani ba, kuma ba za su iya tserewa ba; begensu zai zama na mutuwa.”

< Job 11 >