< Daniel 11 >

1 Y yo mismo, en el primer año de Darío el Medo, tomé mi posición para apoyarlo y defenderlo.
A shekara ta fari ta Dariyus mutumin Mede, na ɗauki matsayina domin in goyi baya in kuma kāre shi.)
2 Así que ahora déjame revelarte la verdad. Todavía hay tres reyes que llegarán al poder en Persia, y luego un cuarto que será mucho más rico que todos los demás. Cuando se haga fuerte por su riqueza, reunirá a todo el reino contra Grecia.
“Yanzu dai, zan faɗa maka gaskiya. Sarakuna uku za su taso a Farisa, sa’an nan kuma na huɗu, wanda zai fi dukansu dukiya. Sa’ad da zai sami iko saboda dukiyarsa, zai zuga dukan kowane mutum yă yi gāba da masarautar Girka.
3 Entonces llegará al poder un rey poderoso. Gobernará con gran autoridad y hará lo que quiera.
Sa’an nan wani babban sarki zai bayyana, wanda zai yi mulki da babban iko yă kuma yi abin da ya ga dama.
4 Pero a medida que extienda su poder, su reino se romperá, se dividirá hacia los cuatro vientos del cielo. No pasará a sus descendientes, y no será gobernada como él lo hizo. Será arrancado y entregado a otros.
Bayan da ya bayyana, daularsa za tă wargaje za a rarraba ta zuwa kusurwoyi huɗu na duniya, a ba waɗansu waɗanda ba zuriyarsa ba, ba kuwa za su yi mulki da iko kamar yadda ya yi ba, gama za a tumɓuki daularsa a kuma ba wa waɗansu.
5 El rey del sur se hará fuerte, pero uno de sus oficiales se hará aún más fuerte y gobernará su reino con gran autoridad.
“Sai sarki Kudu zai yi ƙarfi ƙwarai, amma ɗaya daga cikin komandodinsa zai yi ƙarfi fiye da shi, zai kuma yi mulki masarautarsa da iko mai girma.
6 Algunos años después formarán una alianza, y la hija del rey del sur se casará con el rey del norte para garantizar el tratado de paz. Sin embargo, ella no podrá mantener su poder, ni el poder de él continuar. Ella y sus asistentes serán traicionados, junto con su hijo y su marido. Sin embargo, más tarde,
Bayan’yan shekaru, za su haɗa kai. Diyar sarkin Kudu za tă je wurin sarkin Arewa ta sada zumunci, amma ba za tă riƙe iko ba, shi kuwa da ikonsa ba za su daɗe ba. A waɗannan kwanaki za a bashe ta, da ita da masu rakiyarta da kuma mahaifinta da kuma wanda ya goyi bayanta.
7 un nuevo rey del sur de su familia tomará el relevo. Vendrá a atacar al ejército del rey del norte y entrará en su fortaleza. Luchará contra ellos y vencerá.
“Wani daga cikin zuriyarta zai taso yă ɗauki matsayinta. Zai kai wa sojojin sarkin Arewa hari yă kuma shiga kagararsa; zai yi yaƙi da su yă kuma yi nasara.
8 Además, se llevará con él a Egipto los ídolos de sus dioses, junto con sus costosos objetos de plata y oro. Durante algunos años dejará solo al rey del norte.
Zai ƙwace allolinsu, siffofinsu na ƙarfe da kuma kaya masu daraja na azurfa da na zinariya a kuma kai su Masar. Zai yi’yan shekaru bai kai wa sarkin Arewa yaƙi ba.
9 Entonces el rey del norte marchará hacia el reino del rey del sur, pero tendrá que retirarse a su propia tierra.
Sa’an nan sarkin Arewa zai kai wa sarkin Kudu hari, amma zai janye, yă koma ƙasarsa.
10 Sin embargo, sus hijos se prepararán para la guerra, reuniendo un gran número de tropas. Uno de ellos encabezará una avanzada que se precipita como un río que se desborda, cruzando y avanzando para atacar la fortaleza enemiga.
’Ya’yansa maza za su yi shirin yaƙi za su kuma tattara babbar rundunar sojoji, waɗanda za su yi ta mamayewa kamar rigyawar da ba iya tarewa, kuma za su kai yaƙin har kagararsa.
11 Esto enfurecerá al rey del sur, que saldrá a combatir contra el gran ejército reunido por el rey del norte y lo derrotará.
“Sa’an nan sai sarkin Kudu zai kama hanya da fushi zuwa yaƙi da sarkin Arewa, wanda zai tattara babbar rundunar yaƙi, amma za a ci shi da yaƙi.
12 Después de capturar un ejército tan grande, se sentirá muy orgulloso y matará a miles de personas. Pero este triunfo no durará mucho.
Sa’ad da zai kawar da rundunar, sarkin Kudu zai cika da girman kai zai kuma kashe mutane dubbai, duk da haka ba zai kasance mai nasara ba.
13 Años más tarde, el rey del norte volverá a reunir un ejército aún más numeroso que el anterior, y lo invadirá con este enorme ejército, acompañado de abundantes provisiones.
Sarki Arewa kuma zai ƙara tara babbar rundunar soja, wadda ta fi ta dā girma; bayan waɗansu shekaru kuma, zai tafi yaƙi da babbar rundunar mayaƙa cike da kayan yaƙi.
14 Al mismo tiempo, muchos se rebelarán contra el rey del sur. Hombres violentos de su propio pueblo se rebelarán para que se cumpla esta visión, pero fracasarán.
“A waɗannan lokutan mutane da yawa za su tashi gāba da sarkin Kudu. Amma waɗansu’yan kama-karya za su taso daga jama’arka da niyya su cika abin da wahayin ya ce, amma za a fatattake su.
15 Entonces el rey del norte vendrá y construirá rampas de asedio y capturará una ciudad con fuertes defensas. Las fuerzas del sur no podrán impedirlo; ni siquiera sus mejores tropas podrán resistir el ataque.
Sa’an nan sarkin arewa zai zo ya gina mahaurai a jikin katagar birni don yă ci birnin da yaƙi. Sojojin nan na Kudu kuwa ba za su iya tsayawa ba, ko zaɓaɓɓun jarumawansu ma, gama za su rasa ƙarfin tsayawa.
16 El invasor hará lo que quiera; nadie podrá oponerse a él. Estará en la Tierra Hermosa con el poder de destruirlo.
Wanda ya kai harin zai yi yadda ya ga dama, ba wanda zai iya ja da shi. Zai kafa kansa a Kyakkyawar Ƙasa zai kuma sami ikon da zai hallaka ta.
17 Estará decidido a venir con todo el poder de su reino y hará un tratado de paz con el rey del sur. Para asegurarlo, le dará una hija de mujer para que se case con él con el fin de destruir el reino. Pero ella no tendrá éxito y no lo apoyará.
Zai yunƙura yă zo da ƙarfin dukan masarautarsa zai kuma nemi haɗinkan sarkin Kudu. Zai kuma ba shi diyarsa yă aura don yă lalatar da mulkin, amma shirinsa ba zai yi nasara ba ko yă taimake shi ba.
18 Entonces se volverá para atacar las costas y conquistará a muchos, pero un comandante pondrá fin a su comportamiento arrogante, pagándole por ello.
Sa’an nan zai mai da hankalinsa zuwa ƙasashe a bakin kogi, zai kuma kama da yawansu, amma wani komanda zai kawo ƙarshen faɗin ransa, zai kuma sa faɗin ransa yă koma masa.
19 Volverá a las fortalezas de su tierra, pero tropezará y caerá, y desaparecerá.
Bayan wannan, zai juya ga kagarar ƙasarsa, amma zai yi tuntuɓe yă fāɗi, ba kuwa za a ƙara ganinsa ba.
20 Su sucesor enviará a un recaudador de impuestos para mantener la riqueza real. Sin embargo, en poco tiempo morirá, pero no violentamente ni en batalla.
“Magājinsa zai aiki mai karɓar haraji don darajar masarautarsa. Amma ba da daɗewa ba za a hallaka shi, duk da haka ba da fushi ko cikin yaƙi ba.
21 Le seguirá una persona despreciable a la que no se le dará la majestad real. Tomará el relevo pacíficamente y asumirá el control del reino mediante el engaño.
“Magājin wannan sarki zai zama wani mutumin banza wanda ma bai fito daga gidan sarauta ba. Zai taso ba zato ba tsammani, yă ƙwace sarautar ta hanyar zamba.
22 Grandes ejércitos serán barridos ante él. Serán quebrados, así como el príncipe del acuerdo.
Sa’an nan zai shafe mayaƙa masu yawa a gabansa; zai hallaka har da waɗanda suke mulki na alkawari.
23 Después de hacer una alianza con él, actuará de forma engañosa. Llegará al poder pacíficamente, haciéndose fuerte aunque sólo tenga unos pocos partidarios.
Bayan ƙulla yarjejjeniya da shi, zai yi zamba cikin aminci, kuma zai sami damar hawan mulki da goyon baya mutane kaɗan.
24 Invadirá las partes más ricas de la tierra y hará lo que sus padres y antepasados nunca hicieron: repartirá saqueos, despojos y posesiones. Hará planes para atacar fortalezas, pero sólo por un tiempo.
Sa’ad da yankuna mafi arziki suke ji kome lafiya yake, zai kai musu hari kuma Zai aikata abin da kakanninsa ba su taɓa yi ba. Zai rarraba abin da aka kwaso daga yaƙi, da ganima, da dukiya ga dukan mabiyansa. Zai kuma yi shiri yă kai wa mafaka hari, amma na ɗan lokaci ne kawai.
25 Luego sacará su fuerza y valor para reunir un gran ejército contra el rey del sur. El rey del sur se preparará para la guerra. Combatirá con un ejército grande y poderoso, pero no tendrá éxito a causa de las conspiraciones hechas contra él.
“Tare da babbar rundunar mayaƙa zai yi ƙarfin hali yă far wa sarkin Kudu da yaƙi. Sarkin kudu zai haɗa babbar rundunar soja mai ƙarfi don yaƙin, amma ba zai iya karo da shi ba, domin za a shirya masa maƙarƙashiya.
26 Los más cercanos a él lo destruirá. Su ejército será aniquilado; muchos caerán en la batalla.
Waɗanda suke ci daga tanadin sarki za su yi ƙoƙari su hallaka shi; za a share mayaƙansa, kuma za a kashe mutane masu yawa a yaƙin.
27 Los dos reyes, con malas intenciones, se dirán mentiras mientras se sientan juntos a la misma mesa. Pero sus maquinaciones son inútiles: el final llegará en el momento previsto.
Sarakunan nan biyu sun sa mugunta a ransu. Za su zauna a tebur guda su yi ta shara wa juna ƙarya, amma a banza, gama lokacin da aka ƙayyade bai yi ba tukuna.
28 El rey del norte regresará a su país con toda la riqueza que ha saqueado. Estará decidido a atacar el pueblo del santo acuerdo, y hará todo lo posible para destruirlo antes de regresar a su propio país.
“Sarkin Arewa zai koma ƙasarsa da dukiya mai girma, amma zuciyarsa za tă yi gāba da tsattsarkan alkawari. Zai ɗauki mataki a kan wannan abu sa’an nan yă koma ƙasarsa.
29 En el momento predicho volverá a invadir el sur, pero esta vez no será como antes.
“A ƙayyadadden lokaci zai sāke kai wa Kudu hari, amma a wannan karo abin da zai faru zai sha bamban daga abin da ya faru can baya.
30 Los barcos de Chipre vendrán a atacarlo, asustándolo para que se retire. Pero esto lo hará enloquecer, y atacará a la gente del santo acuerdo, reconociendo a los que abandonan su compromiso con el santo acuerdo.
Jiragen ruwa yammancin bakin teku za su yi gāba da shi, zuciyarsa kuwa za tă yi sanyi. Sa’an nan zai juya ya huce haushinsa a kan tsattsarkan alkawari. Zai komo yă nuna jinƙai ga waɗanda suka juya wa tsattsarkan alkawari baya.
31 Sus fuerzas ocuparán y profanarán la fortaleza del Templo. Pondrán fin al servicio continuo, y establecer una forma de idolatría que causa devastación.
“Mayaƙansa za su taso su ƙazantar da kagarar haikali za su kuma kawar da hadaya ta kullum. Sa’an nan za su kafa abin banƙyama da yake lalatarwa.
32 El rey utilizará la adulación para corromper a quienes rompan el acuerdo solemne, pero el pueblo que conoce a su Dios se mantendrá firme en su resistencia.
Ta wurin daɗin baki zai gurɓata waɗannan da suka karya alkawari, amma mutanen da suka san Allahnsu za su yi tsayin daka su yi jayayya da shi.
33 Los líderes sabios del pueblo enseñarán a muchos, aunque durante un tiempo serán muertos a espada y fuego, o serán encarcelados y robados.
“Waɗanda suke da hikima za su wayar da kan mutane da yawa, duk da haka za a kashe su da takobi, waɗansu da wuta, a washe waɗansu a kai su bauta.
34 Durante este tiempo de persecución recibirán un poco de ayuda, y muchos de los que se unan a ellos no serán sinceros.
Sa’ad da suka fāɗi, za su sami ɗan taimako, mutane da yawa za su haɗa kai da su, amma da munafunci.
35 Algunos de los sabios serán asesinados, para que puedan ser refinados y purificados y limpiados hasta el tiempo del fin, porque el tiempo predicho aún está por venir.
Waɗansu masu hikima za su yi tuntuɓe, don a tsabtacce su, a tsarkake su, su yi tsab, har matuƙar da aka ƙayyade ta yi.
36 El rey hará lo que quiera, alabándose a sí mismo y considerándose más grande que cualquier dios, incluso diciendo cosas escandalosas contra el Dios de los dioses. Tendrá éxito hasta que termine el tiempo de la ira, pues se cumplirá lo que se ha decidido.
“Sarkin zai yi abin da ya ga dama. Zai ɗaukaka yă kuma girmama kansa gaba da kowane allah zai kuma faɗa munanan abubuwa a kan Allahn alloli. Zai yi nasara har sai lokacin hukunci ya cika, gama abin da aka ƙaddara zai cika.
37 No tendrá tiempo para los dioses de sus antepasados, ni para el amado por las mujeres, ni para ningún otro dios, pues se considera más grande que cualquiera de ellos.
Ba zai kula da alloli iyayensa ba ko wanda mata suke sha’awa, balle ma yă ga darajar wani allah, amma zai ɗaukaka kansa gaba da su duka.
38 En cambio, honrará al dios de las fortalezas -un dios desconocido para sus antepasados- dándole ofrendas de oro y plata y piedras preciosas y regalos costosos.
A maimakonsu, zai ɗaukaka allahn kagarai; allahn da kakanninsa ba su ko sani ba, shi ne zai miƙa masa zinariya, da azurfa, da duwatsu masu daraja, da abubuwa masu tsada.
39 Tratará con las fortalezas fuertes con la ayuda de este dios extranjero. Dará riquezas a los que lo reconozcan, haciéndolos gobernantes del pueblo, y repartiendo la tierra a precio de saldo.
Zai kai wa kagarai mafi ƙarfi hari da taimakon baƙon allah zai kuma girmama waɗanda suka yarda da shi zai ba su girma, ya kuma shugabantar da su a kan mutane da yawa, zai raba musu ƙasa ta zama ladansu.
40 En el momento del fin, el rey del sur lo atacará. Pero el rey del norte tomará represalias con fuerza como una tormenta, con carros y jinetes y muchos barcos. Avanzará, barriendo muchas tierras.
“A lokaci ƙarshe sarkin Kudu zai tasar masa da yaƙi, sarkin Arewa kuwa zai tunzura, yă tasar masa da kekunan yaƙi da mahayan dawakai, da jiragen ruwa da yawa. Zai ratsa ƙasashe, yă ci su da yaƙi, yă wuce.
41 Invadirá la Tierra Hermosa y matará a mucha gente allí. Sin embargo, Moab, Edom y la mayoría de los amonitas escaparán a su poder.
Zai kuma mamaye Kyakkyawa Ƙasa. Ƙasashe masu yawa za su fāɗi, amma Edom, Mowab da kuma shugabannin Ammon za su kuɓuta daga hannunsa.
42 Extenderá sus ataques contra diferentes países; ni siquiera la tierra de Egipto podrá escapar.
Zai fadada mulkinsa har zuwa ƙasashe masu yawa; Masar ma ba za tă tsira ba.
43 Adquirirá el oro y la plata y las riquezas de Egipto, gobernando sobre ellos y también sobre los libios y los etíopes.
Zai mallaki dukiyoyi na zinariya, da na azurfa, da dukan abubuwa masu tsada na Masar. Zai kuma ci Libiyawa da Kush da yaƙi.
44 Pero las noticias del este y del norte lo alarmarán, y con furia se dispondrá a destruir y exterminar a muchos pueblos.
Amma labari daga gabas da arewa za su firgita shi, shi kuwa zai ci gaba da yin yaƙi da zafi, yă karkashe mutane da yawa, yă shafe su.
45 Establecerá su campamento real entre el mar y la hermosa montaña sagrada. Pero morirá sin que nadie le ayude.
Zai kafa tentin mulkinsa tsakanin tekunan da suke a kyakkyawan tsauni mai tsarki. Duk da haka zai zo ga ƙarshensa, kuma babu wanda zai taimake shi.

< Daniel 11 >