< 2 Reyes 24 >

1 Durante el reinado de Joaquim, Nabucodonosor, tipo de Babilonia, invadió el país y Joaquim se sometió a él. Pero después de tres años Joaquim se rebeló contra Nabucodonosor.
A zamani Yehohiyakim, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kawo wa ƙasar farmaki, Yehohiyakim dai ya zama abokin tarayyarsa na tsawon shekara uku. Daga baya kuma sai ya canja ra’ayi ya yi wa Nebukadnezzar tawaye.
2 Entonces el Señor envió bandas de asaltantes contra Judá para destruirlos. Vinieron de Babilonia, Harán, Moab y Amón, tal como el Señor había dicho por medio de sus siervos los profetas.
Ubangiji ya aiki maharan Babiloniyawa, da na Arameyawa, da na Mowabawa, da na Ammonawa. Ya aike su su hallaka Yahuda bisa ga maganar Ubangiji wadda ya furta ta bakin bayinsa annabawa.
3 El Señor habló contra Judá para desterrarlos de su presencia a causa de todos los pecados que Manasés había cometido y de la gente inocente que había matado,
Ba shakka waɗannan abubuwa sun faru da Yahuda bisa ga umarnin Ubangiji domin yă kawar da su daga gabansa saboda zunuban Manasse da dukan abin da ya yi,
4 llenando Jerusalén con su sangre. El Señor no estaba dispuesto a perdonar esto.
haɗe da zub da jinin marasa laifi. Gama ya ƙazantar da Urushalima da jinin marasa laifi. Ubangiji kuwa bai yi niyyar yafewa ba.
5 El resto de lo que sucedió en el reinado de Joaquim, y todo lo que hizo, está registrado en el Libro de las Crónicas de los Reyes de Judá.
Game da sauran ayyukan mulkin Yehohiyakim da abubuwan da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
6 Joaquim murió, y su hijo Joaquim lo sucedió como rey.
Yehohiyakim ya huta da kakanninsa. Yehohiyacin ɗansa ya gāje shi.
7 El rey de Egipto no volvió a salir de su país, pues el rey de Babilonia se había apoderado de todo el territorio que le pertenecía, desde el Wadi de Egipto hasta el río Éufrates.
Sarkin Masar bai sāke fita daga ƙasarsa don yaƙi ba domin sarkin Babilon ya mamaye yankin, daga Rafin Masar har zuwa Kogin Yuferites.
8 Joaquim tenía dieciocho años cuando llegó a ser rey, y reinó en Jerusalén durante tres meses. Su madre era Nejustá, hija de Elnatán. Ella era de Jerusalén.
Yehohiyacin yana da shekara goma sha takwas da ya zama sarki, ya kuma yi mulki wata uku a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Nehushta’yar Elnatan, mutuniyar Urushalima.
9 Joaquim hizo lo malo a los ojos del Señor, tal como lo había hecho su padre.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa ya yi.
10 En aquel tiempo los oficiales de Nabucodonosor, rey de Babilonia, atacaron Jerusalén y la sitiaron.
A wannan lokaci, hafsoshin Nebukadnezzar sarkin Babilon suka kawo wa Urushalima yaƙi, suka kuma kewaye ta.
11 Entonces Nabucodonosor, rey de Babilonia, vino en persona mientras sus oficiales estaban sitiando la ciudad.
Nebukadnezzar na Babilon da kansa kuwa ya zo birnin yayinda hafsoshinsa suka kewaye ta.
12 Joaquim, rey de Israel, se rindió al rey de Babilonia, junto con su madre, sus oficiales, sus comandantes y sus funcionarios. Fue en el octavo año de su reinado cuando Nabucodonosor capturó a Joaquim.
Yehohiyacin sarkin Yahuda, da mahaifiyarsa, da masu yi masa hidima, da hakimansa, da kuma fadawansa duk suka miƙa kansu ga Nebukadnezzar. A shekara ta takwas ta mulkin sarkin Babilon, sarkin Babilon ya mai da Yehohiyacin ɗan kurkuku.
13 Nabucodonosor tomó todos los tesoros del Templo del Señor y del palacio real, y cortó todos los objetos de oro que Salomón, rey de Israel, había hecho para el Templo del Señor, como el Señor había dicho que sucedería.
Yadda Ubangiji ya faɗa, Nebukadnezzar ya kwashe dukan dukiyar haikalin Ubangiji, da ta fadan sarki, ya kuma kwashe dukan kayan zinariyar da Solomon sarkin Isra’ila ya ƙera domin haikalin Ubangiji.
14 Deportó a toda Jerusalén, a todos los comandantes y a los soldados experimentados, a todos los artesanos y a los trabajadores del metal, un total de diez mil prisioneros. Sólo quedó la gente muy pobre del país.
Ya kwashi dukan mutanen Urushalima zuwa bauta, ya kwashi dukan fadawa, da mayaƙa, da masu sana’a, da maƙera, yawansu ya kai dubu goma. Ba wanda ya ragu, sai matalautan ƙasar.
15 Se llevó a Joaquim al exilio en Babilonia, así como a la madre del rey y a las esposas del rey y a sus funcionarios y a los principales hombres del país, a todos los deportó de Jerusalén a Babilonia.
Nebukadnezzar ya ɗauki Yehohiyacin ya kai bauta a Babilon. Ya kuma kwashe mahaifiyar sarki, da matansa, da fadawansa, da manyan mutanen ƙasar daga Urushalima ya kai Babilon.
16 El rey de Babilonia también deportó a Babilonia a los siete mil hombres de combate y a los mil artesanos y metalúrgicos, todos ellos fuertes y preparados para la batalla.
Sarkin Babilon kuma ya kwashe dukan mayaƙa dubu bakwai, ƙarfafu, shiryayyu don yaƙi, da masu sana’a, da maƙera dubu ɗaya, ya kai Babilon.
17 El rey de Babilonia nombró rey a Matanías, tío de Joaquim, en su lugar, y le cambió el nombre por el de Sedequías.
Sarkin Babilon ya sa Mattaniya, ɗan’uwan mahaifin Yehohiyacin, ya zama sarki a madadinsa, ya canja masa suna zuwa Zedekiya.
18 Sedequías tenía veintiún años cuando llegó a ser rey, y reinó en Jerusalén durante once años. Su madre se llamaba Jamutal, hija de Jeremías.
Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hamutal’yar Irmiya; mutuniyar Libna.
19 Sus hechos fueron malos a los ojos del Señor, tal como los de Joaquim.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda Yehohiyakim ya yi.
20 Todo esto sucedió en Jerusalén y en Judá, a causa de la ira del Señor, hasta que finalmente los desterró de su presencia. Sedequías se rebeló contra el rey de Babilonia.
Saboda fushin Ubangiji ne dukan waɗannan abubuwa suka faru da Urushalima, da kuma Yahuda, a ƙarshe kuma ya kawar da su daga fuskarsa. To, sai Zedekiya ya yi wa sarkin Babilon tawaye.

< 2 Reyes 24 >