< 2 Crónicas 25 >
1 Amasías tenía veinticinco años cuando llegó a ser rey, y reinó en Jerusalén durante veintinueve años. Su madre se llamaba Joadán y era de Jerusalén.
Amaziya yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Yehoyaddin ce; ita daga Urushalima ne.
2 E hizo lo que era correcto a los ojos del Señor, pero no con total compromiso.
Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, amma ba da dukan zuciyarsa ba.
3 Después de asegurarse de que su gobierno era seguro, ejecutó a los oficiales que habían asesinado a su padre el rey.
Bayan sarauta ta kahu a ƙarƙashinsa, sai ya kashe hafsoshin da suka kashe mahaifinsa sarki.
4 Sin embargo, no mató a sus hijos, como está escrito en la Ley, en el libro de Moisés, donde el Señor ordenó “Los padres no deben ser ejecutados por sus hijos, y los hijos no deben ser ejecutados por sus padres. Cada uno debe morir por su propio pecado”.
Duk da haka bai kashe’ya’yansu maza ba amma ya yi bisa ga abin da yake a rubuce a cikin Doka, a cikin Littafin Musa, inda Ubangiji ya umarta, “Ba za a kashe iyaye saboda’ya’yansu ba; ba kuwa za a kashe’ya’ya saboda iyayensu ba; kowa zai mutu saboda zunubansa ne.”
5 Entonces Amasías convocó al pueblo de Judá para el servicio militar, y los asignó por familias a comandantes de millares y de centenas. También hizo un censo de los mayores de veinte años en todo Judá y Benjamín, y descubrió que había 300.000 hombres de combate de primera categoría que sabían usar la lanza y el escudo.
Amaziya ya tattara mutanen Yahuda ya kuma ba su aiki bisa ga iyalansu, ya ba da aiki ga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, a dukan Yahuda da Benyamin. Ya kuma tattara waɗanda suke’yan shekara ashirin da haihuwa ko fiye ya sami mutane dubu ɗari uku da suke a shirye don aikin soja, da suka isa riƙe māshi da garkuwa.
6 También contrató a 100.000 combatientes de Israel listos para la batalla por cien talentos de plata.
Ya kuma ɗauko sojan haya jarumawa dubu ɗari ɗaya daga Isra’ila a kan talenti ɗari na azurfa.
7 Pero un hombre de Dios se le acercó y le dijo: “¡Majestad, no permita que este ejército de Israel se una a usted, porque el Señor no está con Israel, con estos hijos de Efraín!
Amma mutumin Allah ya zo wurinsa ya ce, “Ya sarki, waɗannan runduna daga Isra’ila ba za su tafi tare da kai ba, gama Ubangiji ba ya tare da Isra’ila, ba ya nan da wani cikin mutanen Efraim.
8 Aunque luchen con valentía, Dios los hará tropezar y caer ante el enemigo, pues Dios tiene el poder de ayudarlos o dejarlos caer”.
Ko da ma ya tafi ya yi faɗa da ƙwazo a cikin yaƙi, Allah zai tumɓuke shi a gaban abokan gāba, gama Allah yana da iko yă taimaka ko yă tumɓuke.”
9 Amasías le preguntó al hombre de Dios: “¿Pero qué hay de los cien talentos de plata que pagué al ejército de Israel?” “¡El Señor puede darte mucho más que eso!”, respondió el hombre de Dios.
Amaziya ya tambayi mutumin Allah ya ce, “Amma game da talenti ɗarin da na biya saboda waɗannan rundunonin Isra’ila fa?” Mutumin Allah ya amsa, “Ubangiji zai ba ka fiye da wannan.”
10 Entonces Amasías despidió al ejército que había contratado de Efraín y lo envió a su casa. Ellos se enojaron mucho con Judá, y regresaron a casa furiosos.
Saboda haka Amaziya ya sallame rundunonin da suka zo daga Efraim, ya kuma mayar da su gida. Suka husata da Yahuda suka koma gida da fushi sosai.
11 Entonces Amasías condujo valientemente su ejército al Valle de la Sal, donde atacaron al ejército edomita de Seír y mataron a diez mil de ellos.
Sa’an nan Amaziya ya yi ƙarfin hali ya jagoranci mayaƙansa zuwa Kwarin Gishiri, inda ya kashe mutanen Seyir dubu goma.
12 El ejército de Judá también capturó a otros diez mil, los llevó a la cima de un acantilado y los arrojó al vacío, matándolos a todos.
Mayaƙan Yahuda suka kuma kama mutane dubu goma da rai, suka ɗauke su zuwa ƙwanƙolin dutsen, suka yi ta tunkuɗa su ƙasa suka yi kaca-kaca.
13 Pero los hombres del ejército que Amasías envió a casa, negándose a dejarlos ir con él a la batalla, asaltaron las ciudades de Judá, desde Samaria hasta Bet-horón. Mataron a tres mil de sus habitantes y se llevaron una gran cantidad de botín.
Ana cikin haka, sai rundunar da Amaziya ya mai da su gida, waɗanda ba a bari suka tafi yaƙin ba, suka kai wa garuruwan Yahuda daga Samariya zuwa Bet-Horon hari. Suka kashe mutane dubu uku suka kwashe ganima mai yawan gaske.
14 Cuando Amasías regresó de matar a los edomitas, trajo los dioses de los pueblos de Seír y los erigió como sus propios dioses, los adoró y les ofreció sacrificios.
Da Amaziya ya dawo daga kisan mutanen Edom, sai ya dawo da allolin mutanen Seyir. Ya kafa su a matsayin allolinsa, ya rusuna musu, ya kuma miƙa musu hadayun ƙonawa.
15 El Señor se enojó con Amasías y le envió un profeta que le dijo: “¿Por qué adoras a los dioses de un pueblo que ni siquiera pudo salvar a su propio pueblo de ti?”
Fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan Amaziya, sai ya aiki wani annabi wurinsa wanda ya ce, “Me ya sa ka nemi shawarar allolin mutanen nan, waɗanda ba za su cece mutanensu daga hannunka ba?”
16 Pero mientras él seguía hablando, el rey le dijo: “¿Te hemos hecho consejero del rey? ¡Detente ahora mismo! ¿Quieres que te derriben?” Entonces el profeta se detuvo, pero dijo: “Sé que Dios ha decidido destruirte, porque has actuado así y te has negado a escuchar mis consejos”.
Tun yana cikin magana, sai sarki ya ce masa, “Yaushe muka naɗa ka mai ba sarki shawara? Rufe mana baki! Me zai hana a kashe ka?” Sai annabin ya yi shiru, amma ya ce, “Na dai sani Allah ya riga ya shirya zai hallaka ka, saboda ka aikata wannan, ba ka kuma saurari shawarata ba.”
17 Entonces Amasías, rey de Judá, se dejó aconsejar por sus consejeros y envió un mensaje al rey de Israel, Joás, hijo de Joacaz, hijo de Jehú. “Ven y enfréntate a mí en la batalla”, lo desafió.
Bayan Amaziya sarkin Yahuda ya nemi shawara mashawartansa, sai ya kalubalanci Yowash ɗan Yehoyahaz, ɗan Yehu, sarkin Isra’ila, “Zo mu gamu fuska da fuska.”
18 Joás, rey de Israel, respondió a Amasías, rey de Judá: “Un cardo del Líbano envió un mensaje a un cedro del Líbano, diciendo: ‘Dale tu hija a mi hijo por esposa’, pero un animal salvaje del Líbano pasó y pisoteó el cardo.
Amma Yowash sarkin Isra’ila ya amsa wa Amaziya sarkin Yahuda ya ce, “Wata ƙaya ce a Lebanon, ta aika da saƙo wa itacen al’ul na Lebanon cewa, ‘Ka ba ɗana’yarka aure.’ Sai wani naman jeji na Lebanon ya zo ya tattake ƙayar.
19 Te dices a ti mismo lo grande que eres por haber derrotado a Edom, presumiendo de ello. Pero quédate en casa. ¿Por qué has de suscitar problemas que te harán caer a ti y a Judá contigo?”
Ka ce wa kanka cewa ka ci Edom da yaƙi, yanzu kuwa kana fariya da ɗaga kai. Amma tsaya dai a gida! Me ya sa kake neman faɗa kana neman fāɗuwarka da ta Yahuda?”
20 Pero Amasías no escuchó, pues Dios iba a entregarlo a sus enemigos porque había elegido adorar a los dioses de Edom.
Amma Amaziya bai saurara ba gama Allah ya yi haka domin yă miƙa su ga Yehowash, domin sun nemi shawarar allolin Edom.
21 Así que Joás, rey de Israel, se preparó para la batalla. Él y Amasías, rey de Judá, se enfrentaron en Bet-semes, en Judá.
Saboda haka Yowash sarkin Isra’ila ya kai yaƙi. Shi da Amaziya sarkin Yahuda suka fuskanci juna a Bet-Shemesh a Yahuda.
22 Judá fue derrotado por Israel; todos huyeron a casa.
Isra’ila ta fatattaki Yahuda, sai kowane mutum ya gudu zuwa gidansa.
23 Joás, rey de Israel, capturó a Amasías, rey de Judá, hijo de Joás, hijo de Ocozías, en Bet Semes. Lo llevó a Jerusalén y derribó la muralla de Jerusalén a lo largo de 400 codos, desde la Puerta de Efraín hasta la Puerta de la Esquina.
Yehowash sarkin Isra’ila ya kama Amaziya sarkin Yahuda, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya a Bet-Shemesh. Sa’an nan Yehowash ya kawo shi Urushalima ya farfasa katangar Urushalima daga Ƙofar Efraim har zuwa Ƙofar Kusurwa, wani sashe mai tsawon ƙafa ɗari shida.
24 Se llevó todo el oro y la plata, y todos los artículos encontrados en el Templo de Dios que habían sido cuidados por Obed-edom y en los tesoros del palacio real, así como algunos rehenes, y luego regresó a Samaria.
Ya kwashe dukan zinariya da azurfa da dukan kayayyakin da aka samu a haikalin Allah waɗanda suke a ƙarƙashin kulawar Obed-Edom, da kaya masu daraja na gidan sarki, da waɗanda aka kamo cikin yaƙi, ya kawo Samariya.
25 Amasías, hijo de Joás, rey de Judá, vivió quince años después de la muerte de Joás, hijo de Joacaz, rey de Israel.
Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya rayu shekara goma sha biyar bayan mutuwar Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila.
26 El resto de lo que hizo Amasías, de principio a fin, está escrito en el Libro de los Reyes de Judá e Israel.
Game da sauran ayyukan mulkin Amaziya, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
27 Después de que Amasías renunció a seguir al Señor, se tramó un complot contra él en Jerusalén, y huyó a Laquis. Pero los conspiradores enviaron hombres a Laquis para perseguirlo, y allí lo mataron.
Sa’ad da Amaziya ya bar bin Ubangiji, aka shirya masa maƙarƙashiya a Urushalima, sai ya gudu zuwa Lakish, amma suka aiki mutane suka bi shi zuwa Lakish, a can suka kashe shi.
28 Lo trajeron de vuelta a caballo y lo enterraron con sus padres en la ciudad de Judá.
Aka dawo da shi a kan doki, aka binne shi tare da kakanninsa a Birnin Yahuda.