< 1 Timoteo 2 >
1 En primer lugar quiero animarte a orar por todos: haz peticiones y agradece en nombre de ellos.
Da farko dai, ina gargaɗe ku cewa a yi roƙe-roƙe, ana addu’o’i, ana yin addu’a a madadin waɗansu da kuma a yi godiya saboda kowane mutum
2 De este mismo modo ora por los reyes y por todo tipo de líderes, para que podamos tener una vida tranquila y pacífica, siempre pensando en Dios y tomando la vida con seriedad.
da sarakuna da dukan masu mulki, domin mu zauna lafiya, rai kuma kwance, muna bin Allah sosai a cikin natsuwa.
3 Esto es bueno, y es lo que agrada a Dios, nuestro Salvador.
Wannan yana da kyau, yakan kuma gamshi Allah Mai Cetonmu,
4 Porque él desea que todos seamos salvos y comprendamos la verdad.
wanda yake so dukan mutane su sami ceto su kuma zo ga sanin gaskiya.
5 Pues hay un Dios, y un mediador entre Dios y la humanidad, el hombre Cristo Jesús.
Gama Allah ɗaya ne, matsakanci kuma ɗaya tsakanin Allah da mutane, shi ne kuwa Kiristi Yesu,
6 Él se entregó a fin de que todos pudiéramos ser rescatados nuevamente, demostrando la evidencia a su debido tiempo.
wanda ya ba da kansa fansa domin dukan mutane, shaidar da aka bayar a daidai lokaci.
7 Fui designado para compartir este mensaje y ser su mensajero, ser un maestro para los extranjeros sobre la fe en Dios y la verdad (no miento, digo la verdad).
Don haka ne aka sa ni mai wa’azi, da manzo kuma, gaskiya nake faɗa, ba ƙarya ba, na kuma zama malami mai koya wa al’ummai al’amarin bangaskiya da kuma na gaskiya.
8 Lo que realmente quiero es que los hombres en todas partes oren a Dios con sinceridad. ¡Sin enojos ni discusiones!
Ina so maza a ko’ina su ɗaga hannuwansu masu tsarki cikin addu’a, ba tare da fushi ko faɗa ba.
9 Del mismo modo, las mujeres deben vestir con prudencia, con modestia y apropiadamente. Deben ser atractivas pero no por su corte de cabello o por el uso de oro, perlas o ropas costosas,
Ina kuma so mata su lura su yi wa kansu adon da ya cancanta, da rigunan da suka dace, ba da adon kitso ko sa kayan zinariya ko lu’ulu’u ko kuma tufafi masu tsada ba,
10 sino por las cosas buenas que hacen, como es apropiado en las mujeres que dicen seguir a Dios.
sai dai su yi ayyuka masu kyan da suka dace da matan da suke masu bauta wa Allah.
11 Las mujeres deben aprender en silencio, respetando su lugar.
Ya kamata mace ta riƙa koyo cikin natsuwa da cikakkiyar biyayya.
12 Yo no permito que las mujeres sean instructoras, o que dominen a los hombres; háganlas permanecer en silencio.
Ban ba mace izini ta koyar ko tă yi mulki a kan namiji ba; sai dai ta zauna shiru.
13 Pues Adán fue creado primero, y luego Eva.
Gama Adamu ne aka fara halitta, sa’an nan Hawwa’u.
14 Adán no fue engañado, pero Eva sí fue engañada por completo, y cayó en pecado.
Ba kuma Adamu ne aka yaudara ba; macen ce aka yaudara ta kuma zama mai zunubi.
15 No obstante, las mujeres serán salvadas por convertirse en madres, siempre y cuando sigan con fe y amor, y vivan vidas prudentes en santidad.
Amma mata Za tă sami ceto za su sami ceto ta wurin haihuwa, in suka ci gaba cikin bangaskiya, ƙauna da kuma tsarki tare da halin sanin ya kamata.