< 1 Reyes 15 >

1 Abías llegó a ser rey de Judá en el año dieciocho del reinado de Jeroboam, hijo de Nabat.
A shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yerobowam ɗan Nebat, Abiyam ya zama sarkin Yahuda,
2 Reinó en Jerusalén durante tres años. Su madre se llamaba Macá, hija de Abisalón.
ya kuma yi mulki a Urushalima shekara uku. Sunan mahaifiyarsa Ma’aka ne,’yar Abisalom.
3 Abías cometió todos los pecados que su padre había cometido antes que él. No estaba totalmente dedicado al Señor su Dios como lo había estado su antepasado David.
Shi ma ya aikata dukan irin zunubai da tsohonsa ya yi. Zuciyarsa ba tă bi Ubangiji Allahnsa, kamar yadda zuciyar Dawuda kakansa ta yi ba.
4 Aun así, por amor a David, el Señor su Dios permitió que sus descendientes siguieran gobernando como una lámpara, un hijo que gobernara después de él y que hiciera fuerte a Jerusalén.
Duk da haka, saboda Dawuda Ubangiji Allahnsa ya ba shi fitila a Urushalima ta wurin ta da wani da ya gāje shi, ta wurinsa kuma Urushalima ta yi ƙarfi.
5 Porque David había hecho lo que era justo ante los ojos del Señor, y no se había desviado de nada de lo que el Señor había ordenado durante toda su vida, excepto en el caso de Urías el hitita.
Gama Dawuda ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, bai kuma fasa kiyaye wani daga umarnan Ubangiji ba dukan kwanakinsa, sai dai a batun Uriya mutumin Hitti.
6 (Roboam y Jeroboam siempre estuvieron en guerra entre sí).
Aka yi yaƙi tsakanin Rehobowam da Yerobowam a duk kwanakin Abiya.
7 El resto de lo que sucedió en el reinado de Abías y todo lo que hizo está registrado en el Libro de las Crónicas de los Reyes de Judá. Abías y Jeroboam siempre estuvieron en guerra entre sí.
Game da sauran ayyukan mulkin Abiyam kuwa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. Aka yi yaƙi tsakanin Abiyam da Yerobowam.
8 Abías murió y fue enterrado en la Ciudad de David. Su hijo Asa lo sucedió como rey.
Sai Abiyam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Asa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
9 Asa llegó a ser rey de Judá en el vigésimo año del reinado de Jeroboam, rey de Israel.
A shekara ta ashirin ta Yerobowam sarkin Isra’ila, Asa ya zama sarkin Yahuda,
10 Reinó en Jerusalén cuarenta y un años. Su abuela se llamaba Macá, hija de Abisalón.
ya yi mulki a Urushalima shekara arba’in da ɗaya. Sunan mahaifiya mahaifiyarsa, Ma’aka ne’yar Abisalom.
11 Asá hizo lo justo a los ojos del Señor, como lo había hecho su antepasado David.
Asa ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar yadda kakansa Dawuda ya yi.
12 Expulsó del país a las prostitutas del culto y se deshizo de todos los ídolos que habían fabricado sus antepasados.
Ya kori dukan maza karuwai na masujadai daga ƙasar, ya kuma yi waje da dukan gumakan da mahaifinsa ya yi.
13 Incluso despidió a su abuela Macá como reina madre, porque había hecho un ídolo repugnante. Asa hizo cortar el ídolo y lo quemó en el valle del Cedrón.
Ya tuɓe mahaifiya mahaifiyarsa Ma’aka daga matsayinta na mahaifiyar sarauniya, gama ta gina ƙazantaccen ginshiƙin Ashera. Asa ya yanke ginshiƙin, ya kuma ƙone shi a Kwarin Kidron.
14 Aunque los altares paganos no fueron removidos, Asá se comprometió completamente con el Señor durante toda su vida.
Ko da yake bai cire masujadai da suke kan tuddai ba, zuciyar Asa ta kasance da aminci ɗungum ga Ubangiji dukan kwanakinsa.
15 Llevó a la casa del Señor la plata y el oro y los demás objetos que él y su padre habían dedicado.
Ya kawo azurfa da zinariya da kayayyakin da shi da mahaifinsa suka keɓe a haikalin Ubangiji.
16 Asá y Basá, rey de Israel, estaban siempre en guerra entre sí.
Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
17 Basá, rey de Israel, atacó a Judá y fortificó Ramá para impedir que la gente viniera o fuera a Asa, rey de Judá.
Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura, ya yi yaƙi da Yahuda, ya kuma gina Rama don yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa, sarkin Yahuda.
18 Entonces Asa tomó toda la plata y el oro que quedaba en los tesoros del Templo del Señor y del palacio real. Lo entregó a sus siervos y los envió a Ben-hadad, hijo de Tabrimón, hijo de Hezión, rey de Harán, que vivía en Damasco, junto con este mensaje:
Sai Asa ya ɗauki dukan azurfa da kuma zinariyar da suka rage a ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma nasa fadan, ya ba da su ga wani shugabansa, ya kuma aika da su zuwa ga Ben-Hadad ɗan Tabrimmon, ɗan Heziyon, sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
19 “Hagamos un tratado entre nosotros, como lo hubo entre mi padre y el tuyo. Mira, te he enviado un regalo de plata y oro. Ve y rompe el tratado con Basá, rey de Israel, para que se retire y me deje en paz”.
Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakanina da kai, kamar yadda ta kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Duba, ina aika maka kyautai na azurfa da na zinariya. Yanzu fa sai ka janye yarjejjeniyarka da Ba’asha sarkin Isra’ila, don yă janye daga gare ni.”
20 Ben Adad aceptó la propuesta de Asá y envió a su ejército con sus comandantes a atacar las ciudades de Israel. Capturaron las ciudades de Ijón, Dan, Abel-Bet-macá y todo Quinéret, incluyendo toda la tierra de Neftalí.
Ben-Hadad ya yarda da maganar Sarki Asa, ya kuma aika shugabannin sojojin mayaƙansa ya yi yaƙi da garuruwan Isra’ila. Ya kame Iyon, Dan, Abel-Bet-Ma’aka da dukan Kinneret, haɗe da Naftali.
21 Cuando Basá se enteró de esto, dejó de fortificar Ramá y se retiró a Tirsa.
Da Ba’asha ya ji haka, sai ya daina ginin Rama, ya janye zuwa Tirza.
22 Entonces el rey Asá emitió un anuncio público en toda Judá, sin excepción. El pueblo obedeció y se llevó las piedras y los maderos que Basá había usado para construir Ramá. El rey Asa utilizó estos materiales de construcción para fortalecer Geba de Benjamín, así como Mizpa.
Sai Sarki Asa ya ba da umarni ga dukan Yahuda, kuma babu wanda aka ware, kowa yă taimaka a kwashe duwatsu da katakan da Ba’asha yake amfani da su daga Rama. Da duwatsu da katakan ne Sarki Asa ya gina Geba a Benyamin da kuma Mizfa.
23 El resto de lo que sucedió en el reinado de Asa, todos sus logros, todo lo que hizo y las ciudades que construyó, están registrados en el Libro de las Crónicas de los Reyes de Judá. Pero cuando envejeció tuvo una enfermedad en los pies.
Game da sauran ayyukan mulkin Asa, dukan nasarorinsa, dukan abin da ya yi, da kuma biranen da ya gina, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. A tsufansa, sai ƙafafunsa suka kamu da cuta.
24 Asa murió y fue enterrado con sus antepasados en la Ciudad de David. Su hijo Josafat lo sucedió como rey.
Sai Asa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a birnin kakansa Dawuda. Sai Yehoshafat ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
25 Nadab, hijo de Jeroboam, se convirtió en rey de Israel en el segundo año del reinado de Asá de Judá. Reinó en Israel durante dos años.
Nadab ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a shekara ta biyu ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila shekara biyu.
26 Sus hechos fueron malos a los ojos del Señor. Siguió los caminos de su padre y cometió los mismos pecados que su padre había hecho cometer a Israel.
Ya yi mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin mahaifinsa da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
27 Basá, hijo de Ahías, de la tribu de Isacar, tramó una rebelión contra él. Basá asesinó a Nadab en la ciudad filistea de Guibetón, mientras Nadab y todo el ejército israelita la asediaban.
Ba’asha ɗan Ahiya na gidan Issakar ya yi maƙarƙashiya gāba da shi, ya buge shi a Gibbeton, a wani garin Filistiyawa, yayinda Nadab da dukan Isra’ila suke wa garin kwanto.
28 Basá mató a Nadab y asumió como rey en el tercer año del reinado del rey Asa de Judá.
Ba’asha ya kashe Nadab a shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma gāje shi a matsayin sarki.
29 Tan pronto como llegó a ser rey, mató a todo el resto de la familia de Jeroboam. No dejó con vida a ninguno de los descendientes de Jeroboam: los destruyó a todos, como el Señor había dicho por medio de su siervo Ahías el silonita.
Nan da nan da ya fara mulki, sai ya kashe dukan iyalin Yerobowam. Bai bar wa Yerobowam wani da rai ba, amma ya hallaka su duka, bisa ga maganar Ubangiji da ya ba wa bawansa Ahiya, mutumin Shilo.
30 Esto sucedió por los pecados que Jeroboam había cometido y había hecho cometer a Israel, y porque había hecho enojar al Señor, el Dios de Israel.
Wannan abu ya faru saboda zunuban da Yerobowam ya yi, ya kuma sa Isra’ila ya yi, kuma saboda ya tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya yi fushi.
31 El resto de lo que sucedió en el reinado de Nadab y todo lo que hizo están registrados en el Libro de las Crónicas de los Reyes de Israel.
Game da sauran ayyukan mulkin Nadab da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
32 Asá y Basá, rey de Israel, estaban siempre en guerra entre sí.
Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
33 Basá, hijo de Ahías, llegó a ser rey de todo Israel en el tercer año del reinado del rey Asá en Judá. Basá reinó en Tirsa durante veinticuatro años.
A shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, Ba’asha ɗan Ahiya ya zama sarkin dukan Isra’ila a Tirza, ya kuma yi sarauta shekara ashirin da huɗu.
34 Perolos hechos de Basáfueron malosa los ojos del Señor y siguió el camino de Jeroboam y su pecado, que él había hecho cometer a Israel.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin Yerobowam da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.

< 1 Reyes 15 >