< 1 Crónicas 12 >

1 La siguiente es una lista de los hombres que se unieron a David cuando estaba en Siclag, todavía escondiéndose de Saúl, hijo de Cis. Eran algunos de los principales guerreros que lucharon del lado de David.
Waɗannan su ne mutanen da suka zo wurin Dawuda a Ziklag, yayinda aka kore shi daga gaban Shawulu ɗan Kish (suna cikin jarumawan da suka taimake shi a yaƙi;
2 Todos ellos eran hábiles arqueros, y podían disparar flechas o hondas con la mano derecha o con la izquierda. Eran parientes de Saúl de la tribu de Benjamín.
suna da baka suna kuma iya harba kibiya, ko majajjawa da hannun dama ko na hagu; su’yan’uwan Shawulu ne daga kabilar Benyamin):
3 Ahiezer era su líder, luego lo fue Joás; los hijos de Semaa de Gugibeá; Jeziel y Pelet los hijos de Azmavet; Beraca; Jehú de Anatot;
Ahiyezer babbansu da Yowash’ya’yan Shema’a maza daga Gibeya; Yeziyel da Felet’ya’yan Azmawet; Beraka, Yehu daga Anatot,
4 Ismaías de Gabaón, (un fuerte guerrero entre los Treinta, y líder sobre los Treinta); Jeremías; Jahaziel; Johanán; Jozabad de Gedera;
da Ishmahiya daga Gibeyon, wani jarumi a cikin Talatin nan, wanda shi ne shugaban Talatin; Irmiya, Yahaziyel, Yohanan, Yozabad daga Gedera,
5 Eluzai; Jerimot; Bealías; Semarías; Sefatías de Haruf.
Eluzai, Yerimot, Beyaliya, Shemariya da Shefatiya daga Haruf;
6 Elcana, Isías, Azareel, Joezer y Jasobeam (quienes eran Coreítas);
Elkana, Isshiya, Azarel, Yoyezer da Yashobeyam daga Kora;
7 Joela y Zebadías, los hijos de Jeroham de Gedor.
da Yoyela da Zebadiya’ya’yan Yeroham maza daga Gedor.
8 Algunos guerreros de la tribu de Gad se pasaron al lado de David cuando éste estaba en la fortaleza del desierto. Eran guerreros fuertes y experimentados, curtidos en la batalla, expertos en el uso de escudos y lanzas. Sus rostros parecían tan fieros como los de los leones, y corrían tan rápido como las gacelas en las montañas.
Sai waɗansu mutanen Gad suka koma suna goyon bayan Dawuda suka kuma haɗa kai da shi a kagararsa a hamada. Su ƙwararrun mayaƙa ne, a shirye don yaƙi, kuma suna iya riƙe garkuwa da māshi. Fuskokinsu kamar fuskoki zakoki, kuma suna da sauri kamar bareyi a kan duwatsu.
9 Ezer el era el líder, Obadías (el segundo), Eliab (el tercero),
Ezer shi ne babba, Obadiya shi ne mai binsa a shugabanci, Eliyab na uku,
10 Mismaná (el cuarto), Jeremías (el quinto),
Mismanna na huɗu, Irmiya na biyar,
11 Atai (el sexto), Eliel (el séptimo),
Attai na shida, Eliyel na bakwai,
12 Johanán (el octavo), Elzabad (el noveno),
Yohanan na takwas, Elzabad na tara,
13 Jeremías (el décimo), Macbanai (el undécimo).
Irmiya na goma da kuma Makbannai na goma sha ɗaya.
14 Estos guerreros de Gad eran oficiales del ejército. El menos hábil de ellos estaba a cargo de 100 hombres; y el mejor estaba a cargo de 1.000.
Waɗannan mutanen Gad shugabannin mayaƙa ne; ƙarami a cikinsu zai iya ƙara da mutum ɗari, kuma babba a cikin zai iya ƙara da dubu.
15 Estos eran los que cruzaban el río Jordán en el primer mes del año, cuando se desborda. Expulsaron a todos los pueblos que vivían en el valle, tanto al este como al oeste.
Su ne suka haye Urdun a wata na farko sa’ad da kogin ya yi ambaliya, suka kuma kori duk mai rai a kwarin, na wajen gabas da na wajen yamma.
16 Otros de las tribus de Benjamín y Judá también vinieron a unirse a David en la fortaleza.
Sauran mutanen Benyamin da waɗansu mutanen Yahuda su ma suka zo wurin Dawuda a kagararsa.
17 David salió a recibirlos y les dijo: “Si han venido en son de paz para ayudarme, podemos ser amigos. Pero si han venido a entregarme a mis enemigos, aunque no he hecho nada malo, que el Dios de nuestros padres vea lo que hacen y los condene”.
Sai Dawuda ya fita don yă tarye su, ya kuma ce musu, “In kun zo wurina da salama, don ku taimake ni, to, ina a shirye in bar ku ku haɗa kai tare da ni. Amma in kun zo don ku bashe ni ga abokan gābana sa’ad da hannuwana ba su da laifi a rikici, bari Allah na kakanninmu yă duba yă kuma shari’anta ku.”
18 Entonces el Espíritu vino sobre Amasai, el líder de los Treinta. “¡Somos tuyos, David, y estamos contigo, hijo de Isaí! Que la paz, la prosperidad y el éxito sean tuyos y de los que te ayuden, porque Dios es el que te ayuda”. Así que David les permitió unirse a él, y los puso al frente de su ejército.
Sai Ruhu ya sauko a kan Amasai, shugaban Talatin nan, sai ya ce, “Mu naka ne, ya Dawuda! Muna tare da kai, ya ɗan Yesse! Nasara, nasara gare ka, nasara kuma ga waɗanda suke taimakonka. Gama Allahnka zai taimake ka.” Saboda haka Dawuda ya karɓe su ya kuma mai da su shugabannin ƙungiyoyin maharansa.
19 Otros se pasaron al lado de David desde la tribu de Manasés y se unieron a él cuando fue con los filisteos a atacar a Saúl. Sin embargo, los jefes filisteos decidieron finalmente despedirlos, diciéndose: “Nos costará la cabeza si nos abandona y se une a su amo Saúl”.
Waɗansu mutanen Manasse suka haɗa kai da Dawuda sa’ad da ya tafi tare da Filistiyawa don yă yaƙi Shawulu (Shi da mutanensa ba su taimaki Filistiyawa ba domin bayan shawarwari, shugabanninsu suka salame shi. Sun ce, “Za mu biya da kawunanmu in ya koma ga maigidansa Shawulu.”)
20 La siguiente es una lista de los hombres de Manasés que se pasaron al lado de David cuando éste regresó a Siclag: Adnas, Jozabad, Jediael, Micael, Jozabad, Eliú y Ziletai, jefes de millares en la tribu de Manasés.
Da Dawuda ya tafi Ziklag, waɗannan mutanen Manasse ne suka haɗa kai da shi. Adna, Yozabad, Yediyayel, Mika’ilu, Yozabad, Elihu da Zilletai, shugabannin ƙungiyoyi na dubu a cikin Manasse.
21 Ellos ayudaron a David contra los asaltantes, pues todos eran guerreros fuertes y experimentados y comandantes del ejército.
Suka taimaki Dawuda a kan ƙungiyoyin hari, gama dukansu jarumawa ne sosai, kuma su shugabanni ne a cikin mayaƙansa.
22 Cada día llegaban hombres para ayudar a David, hasta que tuvo un gran ejército, como el ejército de Dios.
Kowace rana mutane suka riƙa zuwa don su taimaki Dawuda, sai da ya kasance da runduna mai girma, kamar mayaƙan Allah.
23 Esta es la lista del número de guerreros armados que vinieron y se unieron a David en Hebrón para entregarle el reino de Saúl, como había dicho el Señor.
Ga yawan mutanen shiryayyu don yaƙi waɗanda suka zo wurin Dawuda a Hebron don su mai da mulkin Shawulu gare shi, yadda Ubangiji ya faɗa.
24 De la tribu de Judá, 6.800 guerreros con escudos y lanzas.
Mutanen Yahuda, masu riƙe garkuwa da māshi, su 6,800 shiryayyu don yaƙi;
25 De la tribu de Simeón, 7.100 guerreros fuertes.
mutanen Simeyon, jarumawa shiryayyu don yaƙi, su 7,100;
26 De la tribu de Leví, 4.600,
mutanen Lawi, su 4,600,
27 incluyendo a Joiada, jefe de la familia de Aarón, y con él 3.700,
haɗe da Yehohiyada, shugaban iyalin Haruna tare da mutane 3,700,
28 y Sadoc, un joven guerrero fuerte, con 22 miembros de su familia, todos oficiales.
da Zadok, matashi jarumi sosai, tare da shugabanni su 22 daga iyalinsa;
29 De la tribu de Benjamín, de entre los parientes de Saúl, 3.000, la mayoría de los cuales habían permanecido leales a Saúl hasta ese momento.
mutanen Benyamin,’yan’uwan Shawulu, su 3,000, yawanci waɗanda suke biyayya ga gidan Shawulu sai lokacin;
30 De la tribu de Efraín, 20.800 guerreros fuertes, cada uno de ellos muy apreciado en su propio clan.
mutanen Efraim, jarumawa, sanannu cikin gidajensu, su 20 800;
31 De la media tribu de Manasés, 18.000 hombres designados por su nombre para venir a hacer rey a David.
mutanen rabin kabilar Manasse, sanannu da sunaye suka zo suka mai da Dawuda sarki, su 18,000;
32 De la tribu de Isacar vinieron líderes que conocían y podían entender los signos de los tiempos y lo que Israel debía hacer: un total de 200 líderes de la tribu junto con sus parientes.
mutanen Issakar, masu fahimtar lokuta suka kuma san abin da ya kamata Isra’ila ya yi, manya 200, tare da danginsu a ƙarƙashin shugabancinsu;
33 De la tribu de Zabulón, 50.000 guerreros. Estaban completamente armados y listos para la batalla, y totalmente dedicados.
mutanen Zebulun, ƙwararru sojoji shiryayyu don yaƙi da kowane irin makami, suka zo don su taimaki Dawuda da zuciya ɗaya, su 50,000;
34 De la tribu de Neftalí, 1.000 oficiales y 37.000 guerreros con escudos y lanzas.
mutanen Naftali su 1,000 shugabanni, tare da mutane 37,000 masu riƙe garkuwa da masu;
35 De la tribu de Dan, 28.600 guerreros, todos preparados para la batalla.
mutanen Dan, shiryayyu don yaƙi, su 28,600;
36 De la tribu de Aser, 40.000 guerreros experimentados, todos listos para la batalla.
mutanen Asher, ƙwararrun sojoji shiryayyu don yaƙi, su 40,000;
37 De la parte oriental del río Jordán, de las tribus de Rubén, Gad y la media tribu de Manasés, 120.000 guerreros con todo tipo de armas.
kuma daga gabashin Urdun, mutanen Ruben, Gad da kuma rabin kabilar Manasse, masu kayan yaƙi iri-iri, su 120,000.
38 Todos estos hombres llegaron a Hebrón vestidos para la batalla, completamente decididos a hacer rey a David. Todo Israel estaba de acuerdo en que David debía ser rey.
Dukan waɗannan mayaƙa ne waɗanda suka ba da kansu da yardar rai su yi hidima. Suka zo Hebron da cikakken niyya don su naɗa Dawuda sarki a bisa dukan Isra’ila. Duka sauran Isra’ilawa su ma suka goyi baya a naɗa Dawuda sarki.
39 Se quedaron allí tres días, comiendo y bebiendo juntos, pues sus parientes les habían proporcionado provisiones.
Mutanen suka yi kwana uku a can tare da Dawuda, suna ci suna sha, gama iyalansu sun yi musu tanadi.
40 Sus vecinos, incluso de lugares tan lejanos como Isacar, Zabulón y Neftalí, llegaron trayendo comida en burros, camellos, mulas y bueyes. Tenían mucha harina, tortas de higos, racimos de pasas, vino, aceite de oliva, ganado y ovejas, porque Israel estaba muy contento.
Haka ma, maƙwabtansu daga nesa har Issakar, Zebulun da Naftali suka zo suka kawo abinci a kan jakuna, raƙuma, alfadarai da shanu. Akwai tanadin mai yawa na gari, kauɗar ɓaure, nonnan busassun’ya’yan inabi, ruwan inabi, mai, shanu da tumaki. Duk an yi haka don a nuna farin ciki ƙwarai a cikin dukan ƙasar Isra’ila.

< 1 Crónicas 12 >