< Salmos 81 >

1 Al maestro de coro. Por el tono de Hagghittoth (los lagares). De Asaf. Regocijémonos delante de Dios, nuestro Auxiliador; aclamad con júbilo al Dios de Jacob.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
2 Entonad himnos al son del címbalo, la cítara armoniosa y el salterio.
Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
3 Tocad la trompeta en el novilunio y en el plenilunio, nuestro día de fiesta.
Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
4 Porque esta es ley en Israel, prescripción del Dios de Jacob.
wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
5 Como rito recordatorio, la impuso Él a José, cuando salió (Él) contra la tierra de Egipto. Oyó entonces (este) lenguaje nunca escuchado:
Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
6 “Libré sus hombros de la carga, y sus manos dejaron los cestos.
Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
7 En la tribulación me llamaste, y Yo te saqué; te respondí escondido en la nube tempestuosa, te probé en las aguas de Meribá.
Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
8 Oye, pueblo mío, quiero amonestarte. ¡Ojalá me escucharas, oh Israel!
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
9 No haya en ti ningún otro Dios; no te encorves ante un dios ajeno.
Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
10 Soy Yo Yahvé el Dios tuyo, que te saqué de la tierra de Egipto. Abre bien tu boca, y Yo la llenaré.
Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
11 Pero mi pueblo no escuchó mi voz, e Israel no me obedeció.
“Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
12 Por eso los entregué a la dureza de su corazón: a que anduvieran según sus apetitos.
Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
13 ¡Ah, si mi pueblo me oyera! ¡Si Israel siguiera mis caminos!
“A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
14 Cuán pronto humillaría Yo a sus enemigos, y extendería mi mano contra sus adversarios.
da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
15 Los que odian a Dios le rendirían homenaje, y su destino estaría fijado para siempre.
Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
16 Yo le daría a comer la flor del trigo y lo saciaría con miel de la peña.”
Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”

< Salmos 81 >