< Salmos 77 >
1 Al maestro de coro. A Iditún. Salmo de Asaf. Mi voz sube hacia Dios y clama; mi voz va hasta Dios para que me oiga.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
2 En el día de mi angustia busco al Señor; de noche, mis manos se extienden sin descanso, y mi alma rehúsa el consuelo.
Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
3 Si pienso en Dios tengo que gemir; si cavilo, mi espíritu desfallece.
Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
4 Tú mantienes insomnes mis ojos; estoy perturbado, incapaz de hablar.
ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
5 Pienso en los días antiguos y considero los años eternos.
Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
6 Por la noche medito en mi corazón, reflexiono y mi espíritu inquiere:
na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
7 ¿Es que nos desechará el Señor por todos los siglos? ¿No volverá a sernos favorable?
“Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
8 ¿Se habrá agotado para siempre su bondad? ¿Será vana su promesa hecha para todas las generaciones?
Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
9 ¿Se habrá olvidado Dios de su clemencia? o ¿en su ira habrá contenido su misericordia?
Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
10 Y dije: “Este es mi dolor: que la diestra del Altísimo haya cambiado.”
Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
11 Recordaré los hechos de Yahvé; sí, me acuerdo de tus antiguas maravillas;
Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
12 medito todas tus obras y peso tus hazañas.
Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
13 Santo es tu camino, oh Dios, ¿Qué Dios hay tan grande como el Dios nuestro?
Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
14 Tú eres el Dios que obra prodigios, y has dado a conocer a los pueblos tu poder.
Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
15 Redimiste con tu brazo a tu pueblo, a los hijos de Jacob y de José.
Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
16 Las aguas te vieron, oh Dios, te vieron las aguas, y temblaron; hasta los abismos se estremecieron.
Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
17 Aguas derramaron las nubes, los cielos hicieron oír su voz, y volaron tus dardos.
Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
18 Tu trueno sonó en el torbellino, los relámpagos iluminaron el mundo; se conmovió y tembló la tierra.
Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
19 Tu camino se abrió a través del mar, y tus sendas sobre inmensas aguas, sin que aparecieran las huellas de tus pisadas.
Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
20 Y Tú mismo guiaste a tu pueblo como un rebaño, por mano de Moisés y de Aarón.
Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.