< Razodetje 22 +
1 In pokazal mi je čisto reko vode življenja, svetlo kakor kristal, izhajajočo iz prestola Božjega in jagnjetovega.
Sai mala'ika ya nuna mani kogin ruwan rai, ruwa mai tsabta. Yana fitowa daga cikin kursiyin Allah da na Dan-Rago
2 Sredi ulic njegovih in reke tam pa tam drevo življenja, ki dela sadov dvanajst, vsak mesec dajoč sad svoj; in listje drevesovo je v ozdravljenje narodov.
ta tsakiyar titin birnin. A kowanne gefen kogin akwai itacen rai, mai ba da 'ya'ya iri goma sha biyu, kowanne wata. Ganyayen itacen kuma domin warkar da al'ummai ne.
3 In nobenega prokletstva ne bode več; in prestol Božji in jagnjetov bode v njem; in hlapci njegovi bodo mu služili;
Babu sauran la'ana nan gaba. Kursiyin Allah da na Dan Rago za su kasance a cikin birnin, bayinsa kuma za su yi masa bauta.
4 In gledali bodo obličje njegovo, in ime njegovo na njih čelih.
Za su ga fuskarsa, sunansa kuma zai kasance a goshinsu.
5 In noči ne bode tam; in potreba jim ni svetilnice in uči solnčne, ker Gospod Bog jih razsvetljuje; in kraljevali bodo na vekov veke. (aiōn )
Babu sauran dare; ba za su bukaci hasken fitila ko hasken rana ba gama Ubangiji Allah zai haskaka su. Za su yi mulki har abada abadin. (aiōn )
6 In reče mi: Té besede so gotove in resnične; in Gospod, svetih prerokov Bog, poslal je angela svojega, kazat hlapcem svojim, kaj se ima zgoditi hitro.
Mala'ika ya ce mani, “Wadannan kalmomi amintattu ne da gaskiya. Ubangiji, Allah na ruhohin annabawa, ya aiki mala'ikansa ya nuna wa bayinsa abin da lallai zai faru ba da dadewa ba”.
7 Glej, hitro pridem. Blagor mu, kdor hrani besede prerokovanja té knjige!
“Duba! Ina zuwa ba da dadewa ba! Mai albarka ne wanda ya yi biyayya da kalmomin littafin nan.”
8 In jaz Janez sem, ki sem videl to in slišal; in ko sem slišal in videl, padel sem molit pred noge angelove, kateri mi je to kazal.
Ni, Yahaya, nine na ji na kuma ga wadannan abubuwa. Sa'adda na ji na gan su, sai na fadi gaban kafaffun mala'ikan da ya nuna mani wadannan abubuwa domin in yi masa sujada.
9 In reče mi: Nikar! kajti sohlapec sem tvoj in izmed bratov tvojih, prerokov, in njih, ki hranijo besede te knjige; Boga môli.
Ya ce mani, “Kada ka yi haka! Ni abokin bauta ne tare da kai, tare da 'yan'uwanka annabawa, da wadanda ke biyayya da kalmomin littafin nan. Yi sujada ga Allah!”
10 In reče mi: Ne zapečati besed prerokovanja te knjige; ker čas je blizu.
Ya ce mani, “Kada ka rufe kalmomin anabcin littafin nan, gama lokaci ya kusa.
11 Kdor dela krivico, naj jo dela še, in kdor je nesnažen bodi še nesnažen; in pravični opravičuj se še, in sveti naj se še posvečuje.
Wanda yake mara adalci, bari ya cigaba da yin rashin adalci. Wanda yake mai kazanta bari ya cigaba da kazantar da kansa. Wanda yake mai adalci bari ya cigaba da yin adalci. Wanda yake mai-tsarki, bari yaci gaba da tsarki.”
12 In glej, hitro pridem, in plačilo moje z menoj povrnit vsakemu, kakor bode delo njegovo.
“Duba! Ina zuwa ba da dadewa ba. Sakamakona na tare da ni, zan saka wa kowa gwargwadon aikin da ya yi.
13 Jaz sem A in O, začetek in konec, prvi in zadnji.
Nine Alpha da Omega, farko da karshe, mafarin abu da karshensa.
14 Blagor jim, kateri delajo zapovedi njegove, da bode njih oblast do drevesa življenja, in skozi vrata vnidejo v mesto.
Masu albarka ne wadanda suka wanke rigunansu domin su sami izini su ci daga itacen rai su kuma shiga birnin ta kofofinsa.
15 Zunaj pa psi in čarovniki in kurbirji in morilci in malikovalci, in vsak, kdor ljubi in dela laž.
A waje akwai karnuka, masu sihiri, masu bautar gumaka, fasikai, masu kisan kai, da duk wanda yake kaunar aikata rashin gaskiya.
16 Jaz Jezus poslal sem angela svojega, pričat vam to po občinah. Jaz sem korenina in rod Davidov, zvezda svetla in jutranja.
Ni, Yesu na aiko mala'ikana ya shaida maku wadannan abubuwa saboda ikilisiyoyi. Nine tushe da zuriyar Dauda, tauraron asubahi mai-haske.”
17 In Duh in nevesta govorita: Pridi! in kdor sliši, naj reče: Pridi! in kdor je žejen, pridi, in kdor hoče, vzemi vodo življenja zastonj!
Ruhu da Amarya suka ce, “Zo!” Bari wanda ya ji ya ce, “Zo!” Kowanne mai jin kishi, da kowanne mai bukatar ta, bari ya sami ruwan rai kyauta.
18 Pričam namreč vsakemu, kdor sliši besede prerokovanja té knjige: Če temu kdo pridene, njega zadene Bog sè šibami, zapisanimi v tej knjigi.
Ina shaida wa duk mai jin kalmomin anabcin wannan littafi: Idan wani ya kara a kansu, Allah zai kara masa annoban da ke rubuce a cikin littafin.
19 In če kdo odvzame od besed knjige tega prerokovanja, odvzame mu Bog dél njegov od knjige življenja, in iz mesta svetega in kar je pisano v tej knjigi.
Idan wani ya rage daga kalmomin wannan littafin anabci, Allah zai rage rabonsa daga cikin itacen rai daga cikin birni mai-tsarki, wadanda aka rubuta cikin wannan littafi.
20 On, ki to priča, govori: Dà, hitro pridem. Amen, dà, pridi, Gospod Jezus!
Shi wanda ya shaida wadannan abubuwa ya ce, “I! Ina zuwa ba da dadewa ba.” Amin! Zo, Ubangiji Yesu!
21 Milost Gospoda našega Jezusa Kristusa z vami vsemi! Amen.
Alherin Ubangiji Yesu ya kasance tare da kowanne dayanku. Amin.